طه · Juz 16
Tafi zuwa
Alamomi
Mai karantawa / Qārī
Gudun sauti
Maimaita aya
Maimaita
Gungumewa kai
Fassara

Abubakar Mahmoud Gumi

Fontin larabci
Girman rubutu
Larabci
Fassara
Zangin da za a hadda
Maimaitawa
Kowane aya
Cikakken madauki
Babban mai karantawa
A ci gaba - Madauki A-B /

Kara Shafi 313 na Alkur'ani

Shafi 313 na Mushaf yana ɗauke da ayoyi 25. Yana cikin Juz 16, Hizb 32.

An sabunta a 10 Yuli 2026 03h52

Page 313 dans le Coran

25
ayoyi
16
Juz
32
Hizb
1
Surah

Sourate dans la page 313

Juz 16
Shafi 313
سورة طه
Juz 16 54.3% (146/269)
Hizb 32 8.9% (12/135)

وَأَنَا ٱخْتَرْتُكَ فَٱسْتَمِعْ لِمَا يُوحَىٰٓ ﴿١٣﴾

"Kuma Nĩ Nã zãɓe ka. Sai ka saurãra ga abin da ake yin wahayi."

إِنَّنِىٓ أَنَا ٱللَّهُ لَآ إِلَـٰهَ إِلَّآ أَنَا۠ فَٱعْبُدْنِى وَأَقِمِ ٱلصَّلَوٰةَ لِذِكْرِىٓ ﴿١٤﴾

"Lalle, Nĩ Ni ne Allah. Bãbu abin bautawa fãce Ni. Sai ka bauta Mini, kuma ka tsayar da salla dõmin tuna Ni."

إِنَّ ٱلسَّاعَةَ ءَاتِيَةٌ أَكَادُ أُخْفِيهَا لِتُجْزَىٰ كُلُّ نَفْسٍۭ بِمَا تَسْعَىٰ ﴿١٥﴾

"Lalle ne Sa'a mai zuwa ce, lnã kusa da In ɓõye ta dõmin a sãka wa dukan rai da abin da yake aikatãwa."

فَلَا يَصُدَّنَّكَ عَنْهَا مَن لَّا يُؤْمِنُ بِهَا وَٱتَّبَعَ هَوَىٰهُ فَتَرْدَىٰ ﴿١٦﴾

"Sabõda haka, kada wanda bã ya yin ĩmãni da ita kumaya bi son zuciyarsa, ya taushe ka daga gare ta har ka halaka."

وَمَا تِلْكَ بِيَمِينِكَ يَـٰمُوسَىٰ ﴿١٧﴾

"Kuma wãce ce waccan ga dãmanka yã Mũsa!"

قَالَ هِىَ عَصَاىَ أَتَوَكَّؤُا۟ عَلَيْهَا وَأَهُشُّ بِهَا عَلَىٰ غَنَمِى وَلِىَ فِيهَا مَـَٔارِبُ أُخْرَىٰ ﴿١٨﴾

Ya ce: "Ita sandãta ce, inã dõgara a kanta, kuma inã kakkaɓar ganye da ita a kan ƙananan bisãshẽna kuma inã da waɗansu bukãtõci na dabam a gare ta."

قَالَ أَلْقِهَا يَـٰمُوسَىٰ ﴿١٩﴾

Ya ce: "Ka yi jĩfa da ĩta, yã Mũsã!"

فَأَلْقَىٰهَا فَإِذَا هِىَ حَيَّةٌۭ تَسْعَىٰ ﴿٢٠﴾

Sai ya jẽfa ta. Sai gã ta dabbar macĩjiya, tanã tafiya da gaggãwa.

قَالَ خُذْهَا وَلَا تَخَفْ ۖ سَنُعِيدُهَا سِيرَتَهَا ٱلْأُولَىٰ ﴿٢١﴾

Ya ce: "Ka kãma ta kuma kada ka ji tsõro. Za Mu mayar da ita ga hãlinta na farko."

وَٱضْمُمْ يَدَكَ إِلَىٰ جَنَاحِكَ تَخْرُجْ بَيْضَآءَ مِنْ غَيْرِ سُوٓءٍ ءَايَةً أُخْرَىٰ ﴿٢٢﴾

"Kuma ka haɗa hannunka zuwa ga damtsenka, ya fita yanã fari, bãbu sõfane, wata ãyã ta dabam."

لِنُرِيَكَ مِنْ ءَايَـٰتِنَا ٱلْكُبْرَى ﴿٢٣﴾

"Dõmin Mu nũna maka daga ãyõyinMu manya."

ٱذْهَبْ إِلَىٰ فِرْعَوْنَ إِنَّهُۥ طَغَىٰ ﴿٢٤﴾

"Ka tafi zuwa ga Fĩr'auna. Lalle shĩ ya ƙẽtare haddi (da girman kai)."

قَالَ رَبِّ ٱشْرَحْ لِى صَدْرِى ﴿٢٥﴾

Ya ce: "Ya Ubangiji! Ka buɗa mini, ƙirjĩna.

وَيَسِّرْ لِىٓ أَمْرِى ﴿٢٦﴾

"Kuma ka sauƙaƙe mini al'amarĩna."

وَٱحْلُلْ عُقْدَةًۭ مِّن لِّسَانِى ﴿٢٧﴾

"Kuma Ka warware mini wani ƙulli daga harshẽna."

يَفْقَهُوا۟ قَوْلِى ﴿٢٨﴾

"Su fahimci maganãta."

وَٱجْعَل لِّى وَزِيرًۭا مِّنْ أَهْلِى ﴿٢٩﴾

"Kuma Ka sanya mini wani mataimaki daga mutãnena."

هَـٰرُونَ أَخِى ﴿٣٠﴾

"Hãrũna ɗan'uwana."

ٱشْدُدْ بِهِۦٓ أَزْرِى ﴿٣١﴾

"Ka ƙarfafa halittata da shi."

وَأَشْرِكْهُ فِىٓ أَمْرِى ﴿٣٢﴾

"Kuma Ka shigar da shi a cikin al'amarina."

كَىْ نُسَبِّحَكَ كَثِيرًۭا ﴿٣٣﴾

"Dõmin mu tsarkake Ka da yawa."

وَنَذْكُرَكَ كَثِيرًا ﴿٣٤﴾

"Kuma mu tuna Ka da yawa."

إِنَّكَ كُنتَ بِنَا بَصِيرًۭا ﴿٣٥﴾

"Lalle Kai, Ka kasance Mai gani gare mu."

قَالَ قَدْ أُوتِيتَ سُؤْلَكَ يَـٰمُوسَىٰ ﴿٣٦﴾

Ya ce: "Lalle ne, an bã ka rõƙonka, yã Mũsã!"

وَلَقَدْ مَنَنَّا عَلَيْكَ مَرَّةً أُخْرَىٰٓ ﴿٣٧﴾

"Kuma lalle ne haƙĩƙa, Mun yi wata baiwa gare ka a wani lõkacin na dabam."

بسم الله الرحمن الرحيم Jum 24 Muharram
الجمعة 24 محرّم
هلال متناقص Gajimaren Raguwa Rana 25.1 / 29.5
Haske 21%
Wata Sabo a cikin kwana 4
الله أكبر Allah Shi ne Mafi Girma