Abubakar Mahmoud Gumi
Shafi 591 na Mushaf yana ɗauke da ayoyi 32. Yana cikin Juz 30, Hizb 59.
An sabunta a 10 Yuli 2026 03h52
coran.read_full_page : Kara Shafi 591 na Alkur'ani →
وَٱلسَّمَآءِ وَٱلطَّارِقِ ﴿١﴾
Inã rantsuwa da sama da mai aukõwa da dare.
وَمَآ أَدْرَىٰكَ مَا ٱلطَّارِقُ ﴿٢﴾
To, mẽ yã sanar da kai abin da ake cẽwa mai aukõwa da dare?
ٱلنَّجْمُ ٱلثَّاقِبُ ﴿٣﴾
Shi ne taurãron nan mai tsananin haske.
إِن كُلُّ نَفْسٍۢ لَّمَّا عَلَيْهَا حَافِظٌۭ ﴿٤﴾
Bãbu wani rai fãce a kansa akwai wani mai tsaro.
فَلْيَنظُرِ ٱلْإِنسَـٰنُ مِمَّ خُلِقَ ﴿٥﴾
To, mutum ya dũba, daga mẽ aka halittã shi?
خُلِقَ مِن مَّآءٍۢ دَافِقٍۢ ﴿٦﴾
An halittã shi daga wani ruwa mai tunkuɗar jũna.
يَخْرُجُ مِنۢ بَيْنِ ٱلصُّلْبِ وَٱلتَّرَآئِبِ ﴿٧﴾
Yanã fita daga tsakanin tsatso da karankarman ƙirji.
إِنَّهُۥ عَلَىٰ رَجْعِهِۦ لَقَادِرٌۭ ﴿٨﴾
Lalle ne Shi (Allah), ga mayar da shi (mutum), tabbas Mai iyãwa ne.
يَوْمَ تُبْلَى ٱلسَّرَآئِرُ ﴿٩﴾
Rãnar da ake jarrabawar asirai.
فَمَا لَهُۥ مِن قُوَّةٍۢ وَلَا نَاصِرٍۢ ﴿١٠﴾
Saboda haka, bã shi da wani ƙarfi, kuma bã shi da wani mai taimako (da zai iya kãre shi daga azãbar Allah).
وَٱلسَّمَآءِ ذَاتِ ٱلرَّجْعِ ﴿١١﴾
Ina rantsuwa da sama ma'abũciyar ruwa mai kõmãwa yana yankẽwa.
وَٱلْأَرْضِ ذَاتِ ٱلصَّدْعِ ﴿١٢﴾
Da ƙasa ma'abũciyar tsãgẽwa,
إِنَّهُۥ لَقَوْلٌۭ فَصْلٌۭ ﴿١٣﴾
Lalle ne shĩ (Alƙur'ãni), haƙĩƙa magana ce daki-daki
وَمَا هُوَ بِٱلْهَزْلِ ﴿١٤﴾
Kuma shĩ bã bananci bane
إِنَّهُمْ يَكِيدُونَ كَيْدًۭا ﴿١٥﴾
Lalle ne sũ, suna ƙulla kaidi na sõsai.
وَأَكِيدُ كَيْدًۭا ﴿١٦﴾
Kuma Ni, Ina mayar da kaidi (gare su) kamar yadda suke ƙulla kaidi.
فَمَهِّلِ ٱلْكَـٰفِرِينَ أَمْهِلْهُمْ رُوَيْدًۢا ﴿١٧﴾
Saboda haka, ka yi wa kafirai jinkiri, ka dakata musu, sannu-sannu.
سَبِّحِ ٱسْمَ رَبِّكَ ٱلْأَعْلَى ﴿١﴾
Ka tsarkake sũnan Ubangijinka Mafi ɗaukaka.
ٱلَّذِى خَلَقَ فَسَوَّىٰ ﴿٢﴾
Wanda Yã yi halitta sa'an nan Ya daidaita abin halittar.
وَٱلَّذِى قَدَّرَ فَهَدَىٰ ﴿٣﴾
Kuma Wanda Ya ƙaddara (abin da Ya so) sannan Ya shiryar, (da mutum ga hanyar alhẽri da ta sharri).
وَٱلَّذِىٓ أَخْرَجَ ٱلْمَرْعَىٰ ﴿٤﴾
Kuma Wanda Ya fitar da makiyãyã.
فَجَعَلَهُۥ غُثَآءً أَحْوَىٰ ﴿٥﴾
Sa'an nan Ya mayar da ita ƙeƙasassa, baƙa.
سَنُقْرِئُكَ فَلَا تَنسَىٰٓ ﴿٦﴾
Za mu karantar da kai (Alƙur'ãni) sabõda haka bã zã ka mantã (shi) ba.
إِلَّا مَا شَآءَ ٱللَّهُ ۚ إِنَّهُۥ يَعْلَمُ ٱلْجَهْرَ وَمَا يَخْفَىٰ ﴿٧﴾
Fãce abin da Allah Ya so, lalle ne Shi (Allah) Ya san bayyane da abin da yake bõye.
وَنُيَسِّرُكَ لِلْيُسْرَىٰ ﴿٨﴾
Kuma za Mu sauƙaƙe maka (al'amari) zuwa ga (Shari'a) mai sauƙi.
فَذَكِّرْ إِن نَّفَعَتِ ٱلذِّكْرَىٰ ﴿٩﴾
Sabõda baka, ka tunãtar, idan tunatarwa zã ta yi amfãni.
سَيَذَّكَّرُ مَن يَخْشَىٰ ﴿١٠﴾
Wanda yake tsõron (Allah) Zai tuna.
وَيَتَجَنَّبُهَا ٱلْأَشْقَى ﴿١١﴾
Kuma shaƙiyyi, zai nisanceta,
ٱلَّذِى يَصْلَى ٱلنَّارَ ٱلْكُبْرَىٰ ﴿١٢﴾
Wanda zai shiga wutar da tã fi girma.
ثُمَّ لَا يَمُوتُ فِيهَا وَلَا يَحْيَىٰ ﴿١٣﴾
Sa'an nan bã zai mutu ba a cikinta, kuma bã zai rãyu ba.
قَدْ أَفْلَحَ مَن تَزَكَّىٰ ﴿١٤﴾
Lalle ne wanda ya tsarkaka (da ĩmãni) yã sãmu babban rabo.
وَذَكَرَ ٱسْمَ رَبِّهِۦ فَصَلَّىٰ ﴿١٥﴾
Kuma ya ambaci sũnan Ubangijinsa, sa'an nan yã yi salla.