الفجر · Juz 30
Tafi zuwa
Alamomi
Mai karantawa / Qārī
Gudun sauti
Maimaita aya
Maimaita
Gungumewa kai
Fassara

Abubakar Mahmoud Gumi

Fontin larabci
Girman rubutu
Larabci
Fassara
Zangin da za a hadda
Maimaitawa
Kowane aya
Cikakken madauki
Babban mai karantawa
A ci gaba - Madauki A-B /

Kara Shafi 593 na Alkur'ani

Shafi 593 na Mushaf yana ɗauke da ayoyi 23. Yana cikin Juz 30, Hizb 60.

An sabunta a 10 Yuli 2026 03h52

Page 593 dans le Coran

23
ayoyi
30
Juz
60
Hizb
1
Surah

Sourate dans la page 593

Juz 30
Shafi 593
سورة الفجر
Juz 30 56.9% (321/564)
Hizb 60 15.6% (45/288)

وَٱلْفَجْرِ ﴿١﴾

Inã rantsuwa da alfijiri.

وَلَيَالٍ عَشْرٍۢ ﴿٢﴾

Da darũruwa gõma.

وَٱلشَّفْعِ وَٱلْوَتْرِ ﴿٣﴾

Da (adadi na) cikã da (na) mãrã.

وَٱلَّيْلِ إِذَا يَسْرِ ﴿٤﴾

Da dare idan yana shũɗewa.

هَلْ فِى ذَٰلِكَ قَسَمٌۭ لِّذِى حِجْرٍ ﴿٥﴾

Ko a cikin waɗannan akwai abin rantsuwa ga mai hankali (da yake kange shi daga zunubi)?

أَلَمْ تَرَ كَيْفَ فَعَلَ رَبُّكَ بِعَادٍ ﴿٦﴾

Ba ka ga yadda Ubangijinka Ya aikata da Ãdãwa ba?

إِرَمَ ذَاتِ ٱلْعِمَادِ ﴿٧﴾

Iramawa mãsu sakon ƙĩrar jiki.

ٱلَّتِى لَمْ يُخْلَقْ مِثْلُهَا فِى ٱلْبِلَـٰدِ ﴿٨﴾

Waɗanda ba a halitta kwatankwacinsu ba a cikin garũruwa (na dũniya).

وَثَمُودَ ٱلَّذِينَ جَابُوا۟ ٱلصَّخْرَ بِٱلْوَادِ ﴿٩﴾

Da samũdãwa waɗanda suka fasa duwãtsu a cikin Wadi suka yi gidãje)?

وَفِرْعَوْنَ ذِى ٱلْأَوْتَادِ ﴿١٠﴾

Da Fir'auna mai turãku.

ٱلَّذِينَ طَغَوْا۟ فِى ٱلْبِلَـٰدِ ﴿١١﴾

Waɗanda suka ƙẽtare iyãkarsu, a cikin garũruwa?

فَأَكْثَرُوا۟ فِيهَا ٱلْفَسَادَ ﴿١٢﴾

Sabõda haka, suka yawaita yin ɓarna a cikinsu.

فَصَبَّ عَلَيْهِمْ رَبُّكَ سَوْطَ عَذَابٍ ﴿١٣﴾

Sabõda haka Ubangijinka Ya zuba musu bũlãlar azãba.

إِنَّ رَبَّكَ لَبِٱلْمِرْصَادِ ﴿١٤﴾

Lalle ne, Ubangijinka Yana nan a mafaka.

فَأَمَّا ٱلْإِنسَـٰنُ إِذَا مَا ٱبْتَلَىٰهُ رَبُّهُۥ فَأَكْرَمَهُۥ وَنَعَّمَهُۥ فَيَقُولُ رَبِّىٓ أَكْرَمَنِ ﴿١٥﴾

To, amma fa mutum idan Ubangijibsa Ya jarraba shi, wãto Yã girmama shi kuma Ya yi masa ni'ima, sai ya ce: "Ubangijina Ya girmama ni."

وَأَمَّآ إِذَا مَا ٱبْتَلَىٰهُ فَقَدَرَ عَلَيْهِ رِزْقَهُۥ فَيَقُولُ رَبِّىٓ أَهَـٰنَنِ ﴿١٦﴾

Kuma idan Ya jarraba shi, wãto Ya ƙuntata masa abincinsa, sai ya ce: "Ubangijina Ya walãkanta ni."

كَلَّا ۖ بَل لَّا تُكْرِمُونَ ٱلْيَتِيمَ ﴿١٧﴾

A'aha! Bari wannan, ai bã ku girmama marãya!

وَلَا تَحَـٰٓضُّونَ عَلَىٰ طَعَامِ ٱلْمِسْكِينِ ﴿١٨﴾

Bã ku kwaɗaitã wa jũnanku ga (tattalin) abincin matalauci!

وَتَأْكُلُونَ ٱلتُّرَاثَ أَكْلًۭا لَّمًّۭا ﴿١٩﴾

Kuma kuna cin dũkiyar gãdo, ci na tãrãwa.

وَتُحِبُّونَ ٱلْمَالَ حُبًّۭا جَمًّۭا ﴿٢٠﴾

Kuma kuna son dũkiya, so mai yawa.

كَلَّآ إِذَا دُكَّتِ ٱلْأَرْضُ دَكًّۭا دَكًّۭا ﴿٢١﴾

A'aha! Idan aka niƙa ƙasa niƙewa sosai.

وَجَآءَ رَبُّكَ وَٱلْمَلَكُ صَفًّۭا صَفًّۭا ﴿٢٢﴾

Kuma Ubangijinka Ya zo, alhãli malã'iku na jẽre, safũ- safu.

وَجِا۟ىٓءَ يَوْمَئِذٍۭ بِجَهَنَّمَ ۚ يَوْمَئِذٍۢ يَتَذَكَّرُ ٱلْإِنسَـٰنُ وَأَنَّىٰ لَهُ ٱلذِّكْرَىٰ ﴿٢٣﴾

Kuma a ranar nan aka zo da Jahannama. A ranar nan mutum zai yi tunãni. To, inã fa tunãni yake a gare shi!

بسم الله الرحمن الرحيم Jum 24 Muharram
الجمعة 24 محرّم
هلال متناقص Gajimaren Raguwa Rana 25 / 29.5
Haske 21%
Wata Sabo a cikin kwana 4
حسبنا الله ونعم الوكيل Allah Ya isa mana, Shi ne mafi kyawun Mai Kiyaye