Abubakar Mahmoud Gumi
Shafi 602 na Mushaf yana ɗauke da ayoyi 14. Yana cikin Juz 30, Hizb 60.
An sabunta a 10 Yuli 2026 03h52
coran.read_full_page : Kara Shafi 602 na Alkur'ani →
لِإِيلَـٰفِ قُرَيْشٍ ﴿١﴾
Sabõda sãbon ¡uraishawa.
إِۦلَـٰفِهِمْ رِحْلَةَ ٱلشِّتَآءِ وَٱلصَّيْفِ ﴿٢﴾
Sãbonsu na tafiyar hunturu da ta bazara.
فَلْيَعْبُدُوا۟ رَبَّ هَـٰذَا ٱلْبَيْتِ ﴿٣﴾
Sabõda haka sai su bauta wa Ubangijin wannan Gida (Ka'abah).
ٱلَّذِىٓ أَطْعَمَهُم مِّن جُوعٍۢ وَءَامَنَهُم مِّنْ خَوْفٍۭ ﴿٤﴾
wanda Ya ciyar da su (Ya hana su) daga yunwa, kuma Ya amintar da su daga wani tsõro.
أَرَءَيْتَ ٱلَّذِى يُكَذِّبُ بِٱلدِّينِ ﴿١﴾
Shin, ka ga wanda ke ƙaryatãwa game da sakamako?
فَذَٰلِكَ ٱلَّذِى يَدُعُّ ٱلْيَتِيمَ ﴿٢﴾
To, wannan shi ne ke tunkue marãya (daga haƙƙinsa).
وَلَا يَحُضُّ عَلَىٰ طَعَامِ ٱلْمِسْكِينِ ﴿٣﴾
Kuma bã ya kwaaitarwa bisa bãyar da abinci ga matalauci.
فَوَيْلٌۭ لِّلْمُصَلِّينَ ﴿٤﴾
To, bone yã tabbata ga masallata.
ٱلَّذِينَ هُمْ عَن صَلَاتِهِمْ سَاهُونَ ﴿٥﴾
Waɗanda suke masu shagala daga sallarsu.
ٱلَّذِينَ هُمْ يُرَآءُونَ ﴿٦﴾
Waɗanda suke yin riya (ga ayyukansu)
وَيَمْنَعُونَ ٱلْمَاعُونَ ﴿٧﴾
Kuma suna hana taimako.
إِنَّآ أَعْطَيْنَـٰكَ ٱلْكَوْثَرَ ﴿١﴾
Lalle ne Mu, Mun yi maka kyauta mai yawa.
فَصَلِّ لِرَبِّكَ وَٱنْحَرْ ﴿٢﴾
Saboda haka, ka yi salla dõmin Ubangijinka, kuma ka sõke (baiko, wato sukar raƙumi).
إِنَّ شَانِئَكَ هُوَ ٱلْأَبْتَرُ ﴿٣﴾
Lalle mai aibanta ka shi ne mai yankakkiyar albarka.