Abubakar Mahmoud Gumi
Shafi 603 na Mushaf yana ɗauke da ayoyi 14. Yana cikin Juz 30, Hizb 60.
An sabunta a 10 Yuli 2026 03h52
coran.read_full_page : Kara Shafi 603 na Alkur'ani →
قُلْ يَـٰٓأَيُّهَا ٱلْكَـٰفِرُونَ ﴿١﴾
Ka ce: "Ya kũ kãfirai!"
لَآ أَعْبُدُ مَا تَعْبُدُونَ ﴿٢﴾
"Bã zan bautã wa abin da kuke bautã wa ba."
وَلَآ أَنتُمْ عَـٰبِدُونَ مَآ أَعْبُدُ ﴿٣﴾
"Kuma kũ, ba ku zama masu bauta wa abin da nake bautã wa ba."
وَلَآ أَنَا۠ عَابِدٌۭ مَّا عَبَدتُّمْ ﴿٤﴾
"Kuma nĩ ban zama mai bautã wa abin da kuka bautã wa ba."
وَلَآ أَنتُمْ عَـٰبِدُونَ مَآ أَعْبُدُ ﴿٥﴾
"Kuma kũ, ba ku zama mãsu bautã wa abin da nake bautã wa ba."
لَكُمْ دِينُكُمْ وَلِىَ دِينِ ﴿٦﴾
"Addininku na garẽ ku, kuma addinina yanã gare ni."
إِذَا جَآءَ نَصْرُ ٱللَّهِ وَٱلْفَتْحُ ﴿١﴾
Idan taimakon Allah ya zo da cin nasara.
وَرَأَيْتَ ٱلنَّاسَ يَدْخُلُونَ فِى دِينِ ٱللَّهِ أَفْوَاجًۭا ﴿٢﴾
Kuma ka ga mutane suna shiga addinin Allah, ƙungiya-ƙungiya.
فَسَبِّحْ بِحَمْدِ رَبِّكَ وَٱسْتَغْفِرْهُ ۚ إِنَّهُۥ كَانَ تَوَّابًۢا ﴿٣﴾
To, ka yi tasbihi game da gõde wa Ubangijinka, kuma ka nẽme Shi gafara, lalle Shi (Ubangijinka) Ya kasance Mai karɓar tũba ne.
تَبَّتْ يَدَآ أَبِى لَهَبٍۢ وَتَبَّ ﴿١﴾
Hannãye biyu na Abũlahabi sun halaka, kuma ya halaka.
مَآ أَغْنَىٰ عَنْهُ مَالُهُۥ وَمَا كَسَبَ ﴿٢﴾
Dũkiyarsa ba ta tsare masa kõme ba, da abin da ya tãra.
سَيَصْلَىٰ نَارًۭا ذَاتَ لَهَبٍۢ ﴿٣﴾
Zã ya shiga wuta mai hũruwa.
وَٱمْرَأَتُهُۥ حَمَّالَةَ ٱلْحَطَبِ ﴿٤﴾
Tãre da matarsa mai ɗaukar itacen (wuta).
فِى جِيدِهَا حَبْلٌۭ مِّن مَّسَدٍۭ ﴿٥﴾
A cikin kyakkyãwan wuyanta akwai igiya ta kaba (Rãnar ¡iyãma).