النجم · Juz 27
Tafi zuwa
Alamomi
Mai karantawa / Qārī
Gudun sauti
Maimaita aya
Maimaita
Gungumewa kai
Fassara

Abubakar Mahmoud Gumi

Fontin larabci
Girman rubutu
Larabci
Fassara
Zangin da za a hadda
Maimaitawa
Kowane aya
Cikakken madauki
Babban mai karantawa
A ci gaba - Madauki A-B /

Kara Ruku'u 460 na Alkur'ani

Ruku'u 460 daga Surah An-Najm ne (ayoyi 1 zuwa 25). Yana ɗauke da ayoyi 25 kuma yana cikin Juz 27.

An sabunta a 10 Yuli 2026 03h52

Ruku 460 dans le Coran

25
ayoyi
1
Surah
27
Juz
v.1 – v.25
Ayoyi

Sourate dans le Ruku 460

Shafi 526
Ruku'u 460
سورة النجم
Juz 27 19.8% (79/399)
Hizb 53 40.3% (79/196)

وَٱلنَّجْمِ إِذَا هَوَىٰ ﴿١﴾

Inã rantsuwa da taurãron, a lõkacin da ya faku.

مَا ضَلَّ صَاحِبُكُمْ وَمَا غَوَىٰ ﴿٢﴾

Ma'abũcinku bai ɓata ba, kuma bai ƙẽtare haddi ba.

وَمَا يَنطِقُ عَنِ ٱلْهَوَىٰٓ ﴿٣﴾

Kuma bã ya yin magana daga son zuciyarsa.

إِنْ هُوَ إِلَّا وَحْىٌۭ يُوحَىٰ ﴿٤﴾

(Maganarsa) ba ta zamo ba, fãce wahayi ne da ake aikõwa.

عَلَّمَهُۥ شَدِيدُ ٱلْقُوَىٰ ﴿٥﴾

(Malã'ika) mai tsananin ƙarfi ya sanar da shi.

ذُو مِرَّةٍۢ فَٱسْتَوَىٰ ﴿٦﴾

Ma'abũcin ƙarfi da kwarjini, sa'an nan ya daidaita.

وَهُوَ بِٱلْأُفُقِ ٱلْأَعْلَىٰ ﴿٧﴾

Alhãli kuwa yanã a sararin samã mafi aukaka.

ثُمَّ دَنَا فَتَدَلَّىٰ ﴿٨﴾

Sa'an nan ya kusanta, kuma ya matsa zurõwa.

فَكَانَ قَابَ قَوْسَيْنِ أَوْ أَدْنَىٰ ﴿٩﴾

Har ya kasance gwargwadon zirã'i biyu, kõ kuma abin da ya fi kusa.

فَأَوْحَىٰٓ إِلَىٰ عَبْدِهِۦ مَآ أَوْحَىٰ ﴿١٠﴾

Sa'an nan ya yi wahayi zuwa ga bãwan Allah (Muhammadu) da abin da ya faɗa (masa).

مَا كَذَبَ ٱلْفُؤَادُ مَا رَأَىٰٓ ﴿١١﴾

Zũciyar (Annabi) bata ƙaryata abin da ya gani ba.

أَفَتُمَـٰرُونَهُۥ عَلَىٰ مَا يَرَىٰ ﴿١٢﴾

Shin, zã ku yi masa musu a kan abin da yake gani?

وَلَقَدْ رَءَاهُ نَزْلَةً أُخْرَىٰ ﴿١٣﴾

Kuma lalle ya gan shi, haƙĩƙatan, a wani lõkacin saukarsa.

عِندَ سِدْرَةِ ٱلْمُنتَهَىٰ ﴿١٤﴾

A wurin da magaryar tuƙẽwa take.

عِندَهَا جَنَّةُ ٱلْمَأْوَىٰٓ ﴿١٥﴾

A inda taken, nan Aljannar makoma take.

إِذْ يَغْشَى ٱلسِّدْرَةَ مَا يَغْشَىٰ ﴿١٦﴾

Lõkacin da abin da yake rufe magaryar tuƙẽwa ya rufe ta.

مَا زَاغَ ٱلْبَصَرُ وَمَا طَغَىٰ ﴿١٧﴾

Ganinsa bai karkata ba, kuma bai ƙetare haddi ba.

لَقَدْ رَأَىٰ مِنْ ءَايَـٰتِ رَبِّهِ ٱلْكُبْرَىٰٓ ﴿١٨﴾

Lalle, tabbas, (Annabinku) ya ga waɗanda suka fi girma daga ãyõyin Ubangijinsa.

أَفَرَءَيْتُمُ ٱللَّـٰتَ وَٱلْعُزَّىٰ ﴿١٩﴾

Shin, kun ga Lãta da uzza?

وَمَنَوٰةَ ٱلثَّالِثَةَ ٱلْأُخْرَىٰٓ ﴿٢٠﴾

Da (wani gunki wai shi) Manãta, na ukunsu?

أَلَكُمُ ٱلذَّكَرُ وَلَهُ ٱلْأُنثَىٰ ﴿٢١﴾

Ashe, kũ ne da ɗa namiji Shĩ (Allah) kuma da ɗiya mace?

تِلْكَ إِذًۭا قِسْمَةٌۭ ضِيزَىٰٓ ﴿٢٢﴾

Wannan fa ya zama rabo naƙasasshe.

إِنْ هِىَ إِلَّآ أَسْمَآءٌۭ سَمَّيْتُمُوهَآ أَنتُمْ وَءَابَآؤُكُم مَّآ أَنزَلَ ٱللَّهُ بِهَا مِن سُلْطَـٰنٍ ۚ إِن يَتَّبِعُونَ إِلَّا ٱلظَّنَّ وَمَا تَهْوَى ٱلْأَنفُسُ ۖ وَلَقَدْ جَآءَهُم مِّن رَّبِّهِمُ ٱلْهُدَىٰٓ ﴿٢٣﴾

Waɗannan bã kõme ba ne fãce sũnãye, waɗanda kuka ambace su da su, kũ da uwãyenku. Allah bai saukar da wani dalĩli game da su ba. (Kãfirai) bã su biyar kõme fãce zato da abin da rãyukansu ke so, Alhãli kuwa shiriyar ta daga wajen Ubangijinsu, ta jẽ musu (sai suka bar ta suka kõma wa zaton).

أَمْ لِلْإِنسَـٰنِ مَا تَمَنَّىٰ ﴿٢٤﴾

Ko (an fai cẽwa) mutum zai sãmi abin da yake gũri?

فَلِلَّهِ ٱلْـَٔاخِرَةُ وَٱلْأُولَىٰ ﴿٢٥﴾

To, Lãhira da dũniya na Allah kawai ne (wanda ya nẽme su daga wani, yã yi kuskure).

بسم الله الرحمن الرحيم Jum 24 Muharram
الجمعة 24 محرّم
هلال متناقص Gajimaren Raguwa Rana 25 / 29.5
Haske 21%
Wata Sabo a cikin kwana 4
الله أكبر Allah Shi ne Mafi Girma