Abubakar Mahmoud Gumi
Ruku'u 504 daga Surah Nuh ne (ayoyi 1 zuwa 20). Yana ɗauke da ayoyi 20 kuma yana cikin Juz 29.
An sabunta a 10 Yuli 2026 03h52
coran.read_full_page : Kara Ruku'u 504 na Alkur'ani →
يُرْسِلِ ٱلسَّمَآءَ عَلَيْكُم مِّدْرَارًۭا ﴿١١﴾
"Ya sako (girgijen) sama a kanku da ruwa mai ɓuɓɓuga."
وَيُمْدِدْكُم بِأَمْوَٰلٍۢ وَبَنِينَ وَيَجْعَل لَّكُمْ جَنَّـٰتٍۢ وَيَجْعَل لَّكُمْ أَنْهَـٰرًۭا ﴿١٢﴾
"Kuma ya yalwata muku game da dũkiya da ɗiya, Ya sanya muku (albarka) ga gõnaki, kuma Ya sanya muku koguna."
مَّا لَكُمْ لَا تَرْجُونَ لِلَّهِ وَقَارًۭا ﴿١٣﴾
"Me ya sãme ku, bã ku fãtar sãmun natsuwa daga Allah,"
وَقَدْ خَلَقَكُمْ أَطْوَارًا ﴿١٤﴾
"Alhãli kuwa, lalle ne, Ya halitta. ku, a cikin hãlãye?"
أَلَمْ تَرَوْا۟ كَيْفَ خَلَقَ ٱللَّهُ سَبْعَ سَمَـٰوَٰتٍۢ طِبَاقًۭا ﴿١٥﴾
"Ba ku ga yadda Allah Ya halitta wasu sammai bakwai ɗabaƙõƙĩ a kan jũna ba?"
وَجَعَلَ ٱلْقَمَرَ فِيهِنَّ نُورًۭا وَجَعَلَ ٱلشَّمْسَ سِرَاجًۭا ﴿١٦﴾
"Ya sanya watã a cikinsu, yana mai haske, Ya sanya rãnã babbar fitila?"
وَٱللَّهُ أَنۢبَتَكُم مِّنَ ٱلْأَرْضِ نَبَاتًۭا ﴿١٧﴾
"Kuma Allah Ya tsirar da ku daga ƙasa (kamar ganye) tsirarwa."
ثُمَّ يُعِيدُكُمْ فِيهَا وَيُخْرِجُكُمْ إِخْرَاجًۭا ﴿١٨﴾
"Sa'an nan Ya mayar da ku a cikinta, kuma Ya fitar da ku fitarwa."
وَٱللَّهُ جَعَلَ لَكُمُ ٱلْأَرْضَ بِسَاطًۭا ﴿١٩﴾
"Kuma Allah Ya sanya muku ƙasa shimfidaɗɗiya."
لِّتَسْلُكُوا۟ مِنْهَا سُبُلًۭا فِجَاجًۭا ﴿٢٠﴾
"Dõmin ku shiga a cikinta, hanyõyi mãsu fãɗi."