Abubakar Mahmoud Gumi
Ruku'u 541 daga Surah Az-Zalzala ne (ayoyi 1 zuwa 8). Yana ɗauke da ayoyi 8 kuma yana cikin Juz 30.
An sabunta a 10 Yuli 2026 03h52
coran.read_full_page : Kara Ruku'u 541 na Alkur'ani →
إِذَا زُلْزِلَتِ ٱلْأَرْضُ زِلْزَالَهَا ﴿١﴾
Idan aka girgiza ƙasa, girgizawarta.
وَأَخْرَجَتِ ٱلْأَرْضُ أَثْقَالَهَا ﴿٢﴾
Kuma ƙasa ta fitar da kayanta, masu nauyi.
وَقَالَ ٱلْإِنسَـٰنُ مَا لَهَا ﴿٣﴾
Kuma mutum ya ce "Mẽ neya same ta?"
يَوْمَئِذٍۢ تُحَدِّثُ أَخْبَارَهَا ﴿٤﴾
A rãnar nan, zã ta faɗi lãbãrinta.
بِأَنَّ رَبَّكَ أَوْحَىٰ لَهَا ﴿٥﴾
cewa Ubangijinka Ya yi umurni zuwa gare ta.
يَوْمَئِذٍۢ يَصْدُرُ ٱلنَّاسُ أَشْتَاتًۭا لِّيُرَوْا۟ أَعْمَـٰلَهُمْ ﴿٦﴾
A rãnar nan mutane za su fito dabam-dabam domin a nuna musu ayyukansu.
فَمَن يَعْمَلْ مِثْقَالَ ذَرَّةٍ خَيْرًۭا يَرَهُۥ ﴿٧﴾
To, wanda ya aikata (wani aiki) gwargwadon nauyin zarra, na alheri, zai gan shi.
وَمَن يَعْمَلْ مِثْقَالَ ذَرَّةٍۢ شَرًّۭا يَرَهُۥ ﴿٨﴾
Kuma wanda ya aikata gwargwadon nauyin zarra na sharri, zai gan shi.