Abubakar Mahmoud Gumi
Surah Ash-Sharh (الشرح) ita ce surah na Makka ta Alkur'ani tana da ayoyi 8. Ku karanta, ku saurari kuma ku hadda wannan surah tare da kayanmu masu hulɗa.
An sabunta a 10 Yuli 2026 03h52
📖 Karatu minti 1coran.read_full_page : Kara Surah Ash-Sharh →
أَلَمْ نَشْرَحْ لَكَ صَدْرَكَ ﴿١﴾
Ba Mu bũɗa maka zũciyarka ba (dõmin ɗaukar haƙuri da fahimta)?
وَوَضَعْنَا عَنكَ وِزْرَكَ ﴿٢﴾
Kuma Muka saryar maka da nauyinka, Ashe.
ٱلَّذِىٓ أَنقَضَ ظَهْرَكَ ﴿٣﴾
Wanda ya nauyayi bãyanka?
وَرَفَعْنَا لَكَ ذِكْرَكَ ﴿٤﴾
Kuma Muka ɗaukaka maka ambatonka?
فَإِنَّ مَعَ ٱلْعُسْرِ يُسْرًا ﴿٥﴾
To, lalle ne tãre da tsananin nan akwai wani sauƙi.
إِنَّ مَعَ ٱلْعُسْرِ يُسْرًۭا ﴿٦﴾
Lalle ne tãre da tsananin nan akwai wani sauƙi.
فَإِذَا فَرَغْتَ فَٱنصَبْ ﴿٧﴾
Sabõda haka idan ka ƙãre (ibãda) sai ka kafu (kana rõƙon Allah).
وَإِلَىٰ رَبِّكَ فَٱرْغَب ﴿٨﴾
Kuma zuwa ga Ubangijinka ka yi kwaɗayi.