Surah Az-Zalzala (الزلزلة) ita ce surah na Madina ta Alkur'ani tana da ayoyi 8. Ku karanta, ku saurari kuma ku hadda wannan surah tare da kayanmu masu hulɗa.
An sabunta a 05 Agusta 2026 16h34
📖 Karatu minti 1Karanta duka cikakken : Kara Surah Az-Zalzala →
إِذَا زُلْزِلَتِ ٱلْأَرْضُ زِلْزَالَهَا ﴿١﴾
Idan aka girgiza ƙasa, girgizawarta.
وَأَخْرَجَتِ ٱلْأَرْضُ أَثْقَالَهَا ﴿٢﴾
Kuma ƙasa ta fitar da kayanta, masu nauyi.
وَقَالَ ٱلْإِنسَـٰنُ مَا لَهَا ﴿٣﴾
Kuma mutum ya ce "Mẽ neya same ta?"
يَوْمَئِذٍۢ تُحَدِّثُ أَخْبَارَهَا ﴿٤﴾
A rãnar nan, zã ta faɗi lãbãrinta.
بِأَنَّ رَبَّكَ أَوْحَىٰ لَهَا ﴿٥﴾
cewa Ubangijinka Ya yi umurni zuwa gare ta.
يَوْمَئِذٍۢ يَصْدُرُ ٱلنَّاسُ أَشْتَاتًۭا لِّيُرَوْا۟ أَعْمَـٰلَهُمْ ﴿٦﴾
A rãnar nan mutane za su fito dabam-dabam domin a nuna musu ayyukansu.
فَمَن يَعْمَلْ مِثْقَالَ ذَرَّةٍ خَيْرًۭا يَرَهُۥ ﴿٧﴾
To, wanda ya aikata (wani aiki) gwargwadon nauyin zarra, na alheri, zai gan shi.
وَمَن يَعْمَلْ مِثْقَالَ ذَرَّةٍۢ شَرًّۭا يَرَهُۥ ﴿٨﴾
Kuma wanda ya aikata gwargwadon nauyin zarra na sharri, zai gan shi.