الصافات · Juz 23
Tafi zuwa
Alamomi
Mai karantawa / Qārī
Gudun sauti
Maimaita aya
Maimaita
Gungumewa kai
Fassara

Abubakar Mahmoud Gumi

Fontin larabci
Girman rubutu
Larabci
Fassara
Zangin da za a hadda
Maimaitawa
Kowane aya
Cikakken madauki
Babban mai karantawa
A ci gaba - Madauki A-B /

Kara Shafi 446 na Alkur'ani

Shafi 446 na Mushaf yana ɗauke da ayoyi 24. Yana cikin Juz 23, Hizb 45.

An sabunta a 10 Yuli 2026 03h52

Page 446 dans le Coran

24
ayoyi
23
Juz
45
Hizb
1
Surah

Sourate dans la page 446

Juz 23
Shafi 446
سورة الصافات
Juz 23 15.7% (56/357)
Hizb 45 28.0% (56/200)

وَٱلصَّـٰٓفَّـٰتِ صَفًّۭا ﴿١﴾

Inã rantsuwa da mãsu yin sahu-sahu (a cikin salla kõ yãƙi).

فَٱلزَّٰجِرَٰتِ زَجْرًۭا ﴿٢﴾

Sa'an nan mãsu yin tsãwa dõmin gargaɗi.

فَٱلتَّـٰلِيَـٰتِ ذِكْرًا ﴿٣﴾

Sa'an nan da mãsu karãtun abin tunãtarwa.

إِنَّ إِلَـٰهَكُمْ لَوَٰحِدٌۭ ﴿٤﴾

Lalle Abin bautawarku haƙĩƙa ¦aya ne.

رَّبُّ ٱلسَّمَـٰوَٰتِ وَٱلْأَرْضِ وَمَا بَيْنَهُمَا وَرَبُّ ٱلْمَشَـٰرِقِ ﴿٥﴾

Ubangijin sammai da ƙasã da abin da ke tsakãninsu, kuma Ubangijin wurãren fitar rãnã.

إِنَّا زَيَّنَّا ٱلسَّمَآءَ ٱلدُّنْيَا بِزِينَةٍ ٱلْكَوَاكِبِ ﴿٦﴾

Lalle Mũ, Mun ƙãwatãr da sama ta kusa da wata ƙawa, watau taurãri.

وَحِفْظًۭا مِّن كُلِّ شَيْطَـٰنٍۢ مَّارِدٍۢ ﴿٧﴾

Kuma sunã tsari daga dukan Shaiɗan mai tsaurin kai.

لَّا يَسَّمَّعُونَ إِلَى ٱلْمَلَإِ ٱلْأَعْلَىٰ وَيُقْذَفُونَ مِن كُلِّ جَانِبٍۢ ﴿٨﴾

Bã zã su iya saurãre zuwa ga jama'a mafi ɗaukaka (Malã'iku) ba, kuma anã jĩfar su daga kõwane gẽfe.

دُحُورًۭا ۖ وَلَهُمْ عَذَابٌۭ وَاصِبٌ ﴿٩﴾

Dõmin tunkuɗẽwa kuma sunã da wata azãba tabbatacciya.

إِلَّا مَنْ خَطِفَ ٱلْخَطْفَةَ فَأَتْبَعَهُۥ شِهَابٌۭ ثَاقِبٌۭ ﴿١٠﴾

Fãce wanda ya fizgi wata kalma, sai yũla mai haske ta bĩ shi.

فَٱسْتَفْتِهِمْ أَهُمْ أَشَدُّ خَلْقًا أَم مَّنْ خَلَقْنَآ ۚ إِنَّا خَلَقْنَـٰهُم مِّن طِينٍۢ لَّازِبٍۭ ﴿١١﴾

Ka tambaye su: "Shin sũ ne mafi wuya ga halittawa, kõ, kuwa waɗanda Muka halitta?" Lalle Mũ, Mun halitta su daga lãkã mai ɗauri.

بَلْ عَجِبْتَ وَيَسْخَرُونَ ﴿١٢﴾

Ã'a, kã yi mãmãki, alhãli kuwa sunã ta yin izgili.

وَإِذَا ذُكِّرُوا۟ لَا يَذْكُرُونَ ﴿١٣﴾

Kuma idan aka tunãtar da su, bã su tunãwa.

وَإِذَا رَأَوْا۟ ءَايَةًۭ يَسْتَسْخِرُونَ ﴿١٤﴾

Idan suka ga wata ãyã, sai su dinga yin izgili.

وَقَالُوٓا۟ إِنْ هَـٰذَآ إِلَّا سِحْرٌۭ مُّبِينٌ ﴿١٥﴾

Kuma su ce, "Wannnan bã kõme ba, fãce sihiri, ne bayyananne."

أَءِذَا مِتْنَا وَكُنَّا تُرَابًۭا وَعِظَـٰمًا أَءِنَّا لَمَبْعُوثُونَ ﴿١٦﴾

"Shin, idan mun mutu, kuma muka kasance turɓaya da kasũsuwa, ashe, lalle mũ tabbas waɗandaake tãyarwa ne?

أَوَءَابَآؤُنَا ٱلْأَوَّلُونَ ﴿١٧﴾

"Ashe kõ da ubanninmu na farko?"

قُلْ نَعَمْ وَأَنتُمْ دَٰخِرُونَ ﴿١٨﴾

Ka ce: "Na'am alhãli kuwa kunã ƙasƙantattu."

فَإِنَّمَا هِىَ زَجْرَةٌۭ وَٰحِدَةٌۭ فَإِذَا هُمْ يَنظُرُونَ ﴿١٩﴾

Tsãwa guda kawai ce, sai gã su, sunã dũbi.

وَقَالُوا۟ يَـٰوَيْلَنَا هَـٰذَا يَوْمُ ٱلدِّينِ ﴿٢٠﴾

Kuma su ce: "Yã bonenmu! Wannan ita ce rãnar sakamako."

هَـٰذَا يَوْمُ ٱلْفَصْلِ ٱلَّذِى كُنتُم بِهِۦ تُكَذِّبُونَ ﴿٢١﴾

Wannan ita ce rãnar rarrabẽwa wadda kuka kasance kuna ƙaryatãwa.

۞ ٱحْشُرُوا۟ ٱلَّذِينَ ظَلَمُوا۟ وَأَزْوَٰجَهُمْ وَمَا كَانُوا۟ يَعْبُدُونَ ﴿٢٢﴾

Ku tãra waɗanda suka yi zãlunci, da abõkan haɗinsu, da abin da suka kasance sunã bautãwa.

مِن دُونِ ٱللَّهِ فَٱهْدُوهُمْ إِلَىٰ صِرَٰطِ ٱلْجَحِيمِ ﴿٢٣﴾

Wanin Allah, sabõda haka ku shiryar da su zuwa ga hanyar Jahĩm.

وَقِفُوهُمْ ۖ إِنَّهُم مَّسْـُٔولُونَ ﴿٢٤﴾

Kuma ku tsayar da su, lalle su, waɗanda ake yi wa tambaya ne.

بسم الله الرحمن الرحيم Jum 24 Muharram
الجمعة 24 محرّم
هلال متناقص Gajimaren Raguwa Rana 25.1 / 29.5
Haske 20%
Wata Sabo a cikin kwana 4
حسبنا الله ونعم الوكيل Allah Ya isa mana, Shi ne mafi kyawun Mai Kiyaye