Abubakar Mahmoud Gumi
Shafi 523 na Mushaf yana ɗauke da ayoyi 23. Yana cikin Juz 27, Hizb 53.
An sabunta a 10 Yuli 2026 03h52
coran.read_full_page : Kara Shafi 523 na Alkur'ani →
كَذَٰلِكَ مَآ أَتَى ٱلَّذِينَ مِن قَبْلِهِم مِّن رَّسُولٍ إِلَّا قَالُوا۟ سَاحِرٌ أَوْ مَجْنُونٌ ﴿٥٢﴾
Kamar haka dai wani Manzo bai jẽ wa waɗanda ke gabãninsu ba fãce sun ce: "Mai sihiri ne kõ mahaukaci."
أَتَوَاصَوْا۟ بِهِۦ ۚ بَلْ هُمْ قَوْمٌۭ طَاغُونَ ﴿٥٣﴾
shin, sunã yi wa jũna wasiyya da shi ne? Ã'a, sũ dai mutãne ne mãsu girman kai.
فَتَوَلَّ عَنْهُمْ فَمَآ أَنتَ بِمَلُومٍۢ ﴿٥٤﴾
Sai ka jũya daga barinsu, kuma kai ba abin zargi ba ne.
وَذَكِّرْ فَإِنَّ ٱلذِّكْرَىٰ تَنفَعُ ٱلْمُؤْمِنِينَ ﴿٥٥﴾
Kuma ka tunãtar, dõmin tunãtarwa tanã amfãnin mũminai.
وَمَا خَلَقْتُ ٱلْجِنَّ وَٱلْإِنسَ إِلَّا لِيَعْبُدُونِ ﴿٥٦﴾
Kuma Ban halitta aljannu da mutãne ba sai dõmin su bauta Mini.
مَآ أُرِيدُ مِنْهُم مِّن رِّزْقٍۢ وَمَآ أُرِيدُ أَن يُطْعِمُونِ ﴿٥٧﴾
Bã Ni nufln (sãmun) wani arziki daga gare su, Bã Ni nufin su (yi Mini hidimar) ciyar da Ni.
إِنَّ ٱللَّهَ هُوَ ٱلرَّزَّاقُ ذُو ٱلْقُوَّةِ ٱلْمَتِينُ ﴿٥٨﴾
Lalle Allah, Shĩ ne Mai azurtãwa, Mai ĩkon yi, Mai cikakken ƙarfi.
فَإِنَّ لِلَّذِينَ ظَلَمُوا۟ ذَنُوبًۭا مِّثْلَ ذَنُوبِ أَصْحَـٰبِهِمْ فَلَا يَسْتَعْجِلُونِ ﴿٥٩﴾
To, lalle waɗanda suka yi zãlunci sunã da masaki (na ɗĩban zunubi) kamar masakin abõkansu, sabõda haka kada su yi Mini gaggãwa.
فَوَيْلٌۭ لِّلَّذِينَ كَفَرُوا۟ مِن يَوْمِهِمُ ٱلَّذِى يُوعَدُونَ ﴿٦٠﴾
Sabõda haka, bone ya tabbata ga waɗanda suka kãfirta, daga rãnar su wadda aka yi musu alkawari.
وَٱلطُّورِ ﴿١﴾
Inã rantsuwa da ¦ũr (Dũtsen Mũsã).
وَكِتَـٰبٍۢ مَّسْطُورٍۢ ﴿٢﴾
Da wani littãfi rubũtacce.
فِى رَقٍّۢ مَّنشُورٍۢ ﴿٣﴾
A cikin wata takardar fãta shimfiɗaɗɗa.
وَٱلْبَيْتِ ٱلْمَعْمُورِ ﴿٤﴾
Da Gidan da aka rãyar da shi (da ibãda).
وَٱلسَّقْفِ ٱلْمَرْفُوعِ ﴿٥﴾
Da rufin nan da aka ɗaukaka.
وَٱلْبَحْرِ ٱلْمَسْجُورِ ﴿٦﴾
Da tẽkun nan da aka cika (da ruwa).
إِنَّ عَذَابَ رَبِّكَ لَوَٰقِعٌۭ ﴿٧﴾
Lalle, azãbar Ubangijinka, haƙĩƙa, mai aukuwa ce.
مَّا لَهُۥ مِن دَافِعٍۢ ﴿٨﴾
Bã ta da mai tunkuɗẽwa.
يَوْمَ تَمُورُ ٱلسَّمَآءُ مَوْرًۭا ﴿٩﴾
Rãnar da samã ke yin mõtsi tanã kai kãwo.
وَتَسِيرُ ٱلْجِبَالُ سَيْرًۭا ﴿١٠﴾
Kuma duwãtsu nã tafiya sunã shũɗẽwa.
فَوَيْلٌۭ يَوْمَئِذٍۢ لِّلْمُكَذِّبِينَ ﴿١١﴾
To, bone yã tabbata a rãnar nan ga mãsu ƙaryatãwa.
ٱلَّذِينَ هُمْ فِى خَوْضٍۢ يَلْعَبُونَ ﴿١٢﴾
Waɗanda suke a cikin kududdufi sunã wãsã.
يَوْمَ يُدَعُّونَ إِلَىٰ نَارِ جَهَنَّمَ دَعًّا ﴿١٣﴾
Rãnar da zã a tunkuɗa su zuwa wutar Jahannama, tunkuɗãwa.
هَـٰذِهِ ٱلنَّارُ ٱلَّتِى كُنتُم بِهَا تُكَذِّبُونَ ﴿١٤﴾
(A ce musu): "Wannan ita ce wutar da kuka kasance kunã ƙaryatãwa game da ita."