القمر · Juz 27
Tafi zuwa
Alamomi
Mai karantawa / Qārī
Gudun sauti
Maimaita aya
Maimaita
Gungumewa kai
Fassara

Abubakar Mahmoud Gumi

Fontin larabci
Girman rubutu
Larabci
Fassara
Zangin da za a hadda
Maimaitawa
Kowane aya
Cikakken madauki
Babban mai karantawa
A ci gaba - Madauki A-B /

Kara Shafi 531 na Alkur'ani

Shafi 531 na Mushaf yana ɗauke da ayoyi 22. Yana cikin Juz 27, Hizb 53.

An sabunta a 10 Yuli 2026 03h52

Page 531 dans le Coran

22
ayoyi
27
Juz
53
Hizb
2
Surah
Juz 27
Shafi 531
سورة القمر
Juz 27 47.6% (190/399)
Hizb 53 96.9% (190/196)

وَمَآ أَمْرُنَآ إِلَّا وَٰحِدَةٌۭ كَلَمْحٍۭ بِٱلْبَصَرِ ﴿٥٠﴾

Kuma umurninMu bai zamo ba fãce da kalma ɗaya, kamar walƙãwar ido.

وَلَقَدْ أَهْلَكْنَآ أَشْيَاعَكُمْ فَهَلْ مِن مُّدَّكِرٍۢ ﴿٥١﴾

Kuma lalle ne haƙĩƙa, Mun halaka irin gayyarku. To, shin, akwai mai tunãni?

وَكُلُّ شَىْءٍۢ فَعَلُوهُ فِى ٱلزُّبُرِ ﴿٥٢﴾

Kuma kõwane abu, da suka aikata shi, yanã a cikin littattafai.

وَكُلُّ صَغِيرٍۢ وَكَبِيرٍۢ مُّسْتَطَرٌ ﴿٥٣﴾

Kuma dukkan ƙarami da babba, rubutacce ne.

إِنَّ ٱلْمُتَّقِينَ فِى جَنَّـٰتٍۢ وَنَهَرٍۢ ﴿٥٤﴾

Lalle mãsu taƙawa sunã a cikin gidãjen Aljanna da kõguna.

فِى مَقْعَدِ صِدْقٍ عِندَ مَلِيكٍۢ مُّقْتَدِرٍۭ ﴿٥٥﴾

A cikin mazaunin gaskiya, wurin Mai ikon yi, Mai iya zartaswa.

ٱلرَّحْمَـٰنُ ﴿١﴾

(Allah) Mai rahama.

عَلَّمَ ٱلْقُرْءَانَ ﴿٢﴾

Yã sanar da Alƙur'ani.

خَلَقَ ٱلْإِنسَـٰنَ ﴿٣﴾

Yã halitta mutum.

عَلَّمَهُ ٱلْبَيَانَ ﴿٤﴾

Yã sanar da shi bayãni (magana).

ٱلشَّمْسُ وَٱلْقَمَرُ بِحُسْبَانٍۢ ﴿٥﴾

Rãnã da watã a kan lissãfi suke.

وَٱلنَّجْمُ وَٱلشَّجَرُ يَسْجُدَانِ ﴿٦﴾

Kuma tsirrai mãsu yãɗo da itãce sunã tawãlu'i.

وَٱلسَّمَآءَ رَفَعَهَا وَوَضَعَ ٱلْمِيزَانَ ﴿٧﴾

Kuma samã Ya ɗaukaka ta, Kuma Yã aza sikẽli.

أَلَّا تَطْغَوْا۟ فِى ٱلْمِيزَانِ ﴿٨﴾

Dõmin kada ku karkatar da sikẽlin.

وَأَقِيمُوا۟ ٱلْوَزْنَ بِٱلْقِسْطِ وَلَا تُخْسِرُوا۟ ٱلْمِيزَانَ ﴿٩﴾

Kuma ku daidaita awo da ãdalci, kuma kada ku rage sikẽlin.

وَٱلْأَرْضَ وَضَعَهَا لِلْأَنَامِ ﴿١٠﴾

Kuma ƙasã Yã aza ta dõmin tãlikai.

فِيهَا فَـٰكِهَةٌۭ وَٱلنَّخْلُ ذَاتُ ٱلْأَكْمَامِ ﴿١١﴾

A cikinta akwai 'ya'yan itãcen marmari da dabĩno mai kwasfa.

وَٱلْحَبُّ ذُو ٱلْعَصْفِ وَٱلرَّيْحَانُ ﴿١٢﴾

Da ƙwãya mai sõshiya da ƙamshi.

فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ ﴿١٣﴾

To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangjinku kuke ƙaryatãwa?

خَلَقَ ٱلْإِنسَـٰنَ مِن صَلْصَـٰلٍۢ كَٱلْفَخَّارِ ﴿١٤﴾

Yã halitta mutum daga ƙẽkasasshen yumɓu kumar kasko.

وَخَلَقَ ٱلْجَآنَّ مِن مَّارِجٍۢ مِّن نَّارٍۢ ﴿١٥﴾

Kuma ya halitta aljani daga bira daga wutã.

فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ ﴿١٦﴾

To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

بسم الله الرحمن الرحيم Jum 24 Muharram
الجمعة 24 محرّم
هلال متناقص Gajimaren Raguwa Rana 25 / 29.5
Haske 21%
Wata Sabo a cikin kwana 4
الحمد لله Alhamdulillah - Godiya ta tabbata ga Allah