المدثر · Juz 29
Tafi zuwa
Alamomi
Mai karantawa / Qārī
Gudun sauti
Maimaita aya
Maimaita
Gungumewa kai
Fassara

Abubakar Mahmoud Gumi

Fontin larabci
Girman rubutu
Larabci
Fassara
Zangin da za a hadda
Maimaitawa
Kowane aya
Cikakken madauki
Babban mai karantawa
A ci gaba - Madauki A-B /

Kara Shafi 576 na Alkur'ani

Shafi 576 na Mushaf yana ɗauke da ayoyi 30. Yana cikin Juz 29, Hizb 58.

An sabunta a 10 Yuli 2026 03h52

Page 576 dans le Coran

30
ayoyi
29
Juz
58
Hizb
1
Surah

Sourate dans la page 576

Juz 29
Shafi 576
سورة المدثر
Juz 29 62.9% (271/431)
Hizb 58 28.9% (65/225)

إِنَّهُۥ فَكَّرَ وَقَدَّرَ ﴿١٨﴾

Lalle ne, Shi, yã yi tunãni, kuma yã ƙaddara (abin da zai faɗã game da Alƙur'ãni)

فَقُتِلَ كَيْفَ قَدَّرَ ﴿١٩﴾

Sabõda haka, aka la'ane shi, kamar yadda ya ƙaddara.

ثُمَّ قُتِلَ كَيْفَ قَدَّرَ ﴿٢٠﴾

Sa'an nan, aka la'ane shi kamar yadda ya ƙaddara.

ثُمَّ نَظَرَ ﴿٢١﴾

Sa'an nan, ya yi tunãni

ثُمَّ عَبَسَ وَبَسَرَ ﴿٢٢﴾

Sa'an nan, ya gintse huska? kuma ya yi murtuk.

ثُمَّ أَدْبَرَ وَٱسْتَكْبَرَ ﴿٢٣﴾

Sa'an nan, ya jũya bãya, kuma ya bunƙãsa,

فَقَالَ إِنْ هَـٰذَآ إِلَّا سِحْرٌۭ يُؤْثَرُ ﴿٢٤﴾

Sai ya ce: "Wannan abu dai bã kõme ba ne fãce wani sihiri, wanda aka ruwaito."

إِنْ هَـٰذَآ إِلَّا قَوْلُ ٱلْبَشَرِ ﴿٢٥﴾

"Wannan maganar mutum dai ce."

سَأُصْلِيهِ سَقَرَ ﴿٢٦﴾

Zã Ni ƙõna shi da Saƙar.

وَمَآ أَدْرَىٰكَ مَا سَقَرُ ﴿٢٧﴾

Kuma mẽ ya sanar da kai abin da akẽ cẽwa Saƙar!

لَا تُبْقِى وَلَا تَذَرُ ﴿٢٨﴾

Bã ta ragẽwa, kuma bã ta bari.

لَوَّاحَةٌۭ لِّلْبَشَرِ ﴿٢٩﴾

Mai nãcẽwa ga jiki ce (da (ƙũna).

عَلَيْهَا تِسْعَةَ عَشَرَ ﴿٣٠﴾

A kanta akwai (matsara) gõma shã tara.

وَمَا جَعَلْنَآ أَصْحَـٰبَ ٱلنَّارِ إِلَّا مَلَـٰٓئِكَةًۭ ۙ وَمَا جَعَلْنَا عِدَّتَهُمْ إِلَّا فِتْنَةًۭ لِّلَّذِينَ كَفَرُوا۟ لِيَسْتَيْقِنَ ٱلَّذِينَ أُوتُوا۟ ٱلْكِتَـٰبَ وَيَزْدَادَ ٱلَّذِينَ ءَامَنُوٓا۟ إِيمَـٰنًۭا ۙ وَلَا يَرْتَابَ ٱلَّذِينَ أُوتُوا۟ ٱلْكِتَـٰبَ وَٱلْمُؤْمِنُونَ ۙ وَلِيَقُولَ ٱلَّذِينَ فِى قُلُوبِهِم مَّرَضٌۭ وَٱلْكَـٰفِرُونَ مَاذَآ أَرَادَ ٱللَّهُ بِهَـٰذَا مَثَلًۭا ۚ كَذَٰلِكَ يُضِلُّ ٱللَّهُ مَن يَشَآءُ وَيَهْدِى مَن يَشَآءُ ۚ وَمَا يَعْلَمُ جُنُودَ رَبِّكَ إِلَّا هُوَ ۚ وَمَا هِىَ إِلَّا ذِكْرَىٰ لِلْبَشَرِ ﴿٣١﴾

Kuma ba Mu sanya ma'abũta wutã (wãto matsaranta) ba, fãce malã'iku, kuma ba Mu sanya adadinsu (gõma sha tara) ba, fãce dõmin fitina ga waɗanda suka kãfirta domin waɗanda aka bai wa littãfi su sãmi yaƙĩni kuma waɗanda suka yi ĩmãni su ƙãra ĩmãni, kuma waɗanda aka bai wa littãfi da mũminai bã zã su yi shakka ba, kuma domin wa ɗanda a cikin zukatansu akwai wata cuta da kãfirai su ce: "Mẽ Allah Yake nufi da wannan, ya kasance misãli?" Haka dai Allah ke ɓatar da wanda Ya so, kuma Ya shiryar da wanda ya so. Kuma bãbu wanda ya san mayãƙan Ubangijinka fãce Shi, kuma ita (wutar) ba ta kasance ba fãce wata tunãtarwa ce ga mutum.

كَلَّا وَٱلْقَمَرِ ﴿٣٢﴾

A'aha! Ina rantsuwa da watã.

وَٱلَّيْلِ إِذْ أَدْبَرَ ﴿٣٣﴾

Da dare a lõkacin da ya jũyar da baya.

وَٱلصُّبْحِ إِذَآ أَسْفَرَ ﴿٣٤﴾

Da sãfiya idan ta wãye.

إِنَّهَا لَإِحْدَى ٱلْكُبَرِ ﴿٣٥﴾

Ita (wutar) ɗayan manyan masĩfũ? ce.

نَذِيرًۭا لِّلْبَشَرِ ﴿٣٦﴾

Mai gargaɗĩ ce ga mutum.

لِمَن شَآءَ مِنكُمْ أَن يَتَقَدَّمَ أَوْ يَتَأَخَّرَ ﴿٣٧﴾

Ga wanda ya so, daga cikinku, ya gabãta ko ya jinkirta.

كُلُّ نَفْسٍۭ بِمَا كَسَبَتْ رَهِينَةٌ ﴿٣٨﴾

Kõwane rai ga abin da ya aikata jingina ce.

إِلَّآ أَصْحَـٰبَ ٱلْيَمِينِ ﴿٣٩﴾

Fãce mutãnen dãma.

فِى جَنَّـٰتٍۢ يَتَسَآءَلُونَ ﴿٤٠﴾

A cikin Aljanna suna tambayar jũna.

عَنِ ٱلْمُجْرِمِينَ ﴿٤١﴾

Game da mãsu laifi.

مَا سَلَكَكُمْ فِى سَقَرَ ﴿٤٢﴾

(Su ce musu) "Me ya shigar da ku a cikin Saƙar?"

قَالُوا۟ لَمْ نَكُ مِنَ ٱلْمُصَلِّينَ ﴿٤٣﴾

Suka ce: "Ba mu kasance munã a cikin mãsu salla ba."

وَلَمْ نَكُ نُطْعِمُ ٱلْمِسْكِينَ ﴿٤٤﴾

"Kuma ba mu kasance muna ciyar da matalautã ba."

وَكُنَّا نَخُوضُ مَعَ ٱلْخَآئِضِينَ ﴿٤٥﴾

"Kuma mun kasance muna kũtsãwa tãre da mãsu kũtsãwa."

وَكُنَّا نُكَذِّبُ بِيَوْمِ ٱلدِّينِ ﴿٤٦﴾

"Mun kasance munã ƙaryata rãnar sãkamako."

حَتَّىٰٓ أَتَىٰنَا ٱلْيَقِينُ ﴿٤٧﴾

"Har gaskiya (wãto mutuwa) ta zo mana."

بسم الله الرحمن الرحيم Jum 24 Muharram
الجمعة 24 محرّم
هلال متناقص Gajimaren Raguwa Rana 25.2 / 29.5
Haske 20%
Wata Sabo a cikin kwana 4
أستغفر الله Ina neman gafara daga Allah