الانسان · Juz 29
Tafi zuwa
Alamomi
Mai karantawa / Qārī
Gudun sauti
Maimaita aya
Maimaita
Gungumewa kai
Fassara

Abubakar Mahmoud Gumi

Fontin larabci
Girman rubutu
Larabci
Fassara
Zangin da za a hadda
Maimaitawa
Kowane aya
Cikakken madauki
Babban mai karantawa
A ci gaba - Madauki A-B /

Kara Shafi 580 na Alkur'ani

Shafi 580 na Mushaf yana ɗauke da ayoyi 25. Yana cikin Juz 29, Hizb 58.

An sabunta a 10 Yuli 2026 03h52

Page 580 dans le Coran

25
ayoyi
29
Juz
58
Hizb
2
Surah
Juz 29
Shafi 580
سورة الانسان
Juz 29 87.0% (375/431)
Hizb 58 75.1% (169/225)

وَمِنَ ٱلَّيْلِ فَٱسْجُدْ لَهُۥ وَسَبِّحْهُ لَيْلًۭا طَوِيلًا ﴿٢٦﴾

Daga dare, sai ka yi sujũda gare Shi, kuma ka tsarkake Shi darẽ mai tsawo.

إِنَّ هَـٰٓؤُلَآءِ يُحِبُّونَ ٱلْعَاجِلَةَ وَيَذَرُونَ وَرَآءَهُمْ يَوْمًۭا ثَقِيلًۭا ﴿٢٧﴾

Lalle ne, waɗannan suna son mai gaugãwa (dũniya) kuma suna bari, a bãyansu, wani yini mai nauyi.

نَّحْنُ خَلَقْنَـٰهُمْ وَشَدَدْنَآ أَسْرَهُمْ ۖ وَإِذَا شِئْنَا بَدَّلْنَآ أَمْثَـٰلَهُمْ تَبْدِيلًا ﴿٢٨﴾

Mũ ne Muka halitta su kuma Muka, ƙarfafa halittarsu, kuma idan Mun so, za Mu musanyâ su da wasu mutane kwatankwacinsu, musanyawa.

إِنَّ هَـٰذِهِۦ تَذْكِرَةٌۭ ۖ فَمَن شَآءَ ٱتَّخَذَ إِلَىٰ رَبِّهِۦ سَبِيلًۭا ﴿٢٩﴾

Lalle ne, wannan wata tunãtarwa ce, saboda wanda ya so ya riƙa hanyar kirki zuwa ga Ubangijinsa.

وَمَا تَشَآءُونَ إِلَّآ أَن يَشَآءَ ٱللَّهُ ۚ إِنَّ ٱللَّهَ كَانَ عَلِيمًا حَكِيمًۭا ﴿٣٠﴾

Kuma, bã zã ku so ba, sai Allah Ya so, lalle ne Allah Yã kasance Masani' Mai hikima.

يُدْخِلُ مَن يَشَآءُ فِى رَحْمَتِهِۦ ۚ وَٱلظَّـٰلِمِينَ أَعَدَّ لَهُمْ عَذَابًا أَلِيمًۢا ﴿٣١﴾

Yana shigar da wanda Ya so a cikin rahamarsa, kuma azzãlumai, Yã yi musu tattalin wata azãba mai raɗaɗi.

وَٱلْمُرْسَلَـٰتِ عُرْفًۭا ﴿١﴾

Ina rantsuwa da iskõkin da ake sakõwa jẽre, sunã bin jũna.

فَٱلْعَـٰصِفَـٰتِ عَصْفًۭا ﴿٢﴾

Sa'an nan, su zamã iskõki mãsu ƙarfi suna kaɗãwa da ƙarfi.

وَٱلنَّـٰشِرَٰتِ نَشْرًۭا ﴿٣﴾

Kuma, mãsu watsa rahama wãtsãwa.

فَٱلْفَـٰرِقَـٰتِ فَرْقًۭا ﴿٤﴾

sa'an nan, da ãyõyi mãsu rarrabe gaskiya da ƙarya rarrabẽwa.

فَٱلْمُلْقِيَـٰتِ ذِكْرًا ﴿٥﴾

Sa'an nan da malã'iku mãsu jẽfa tunãtarwa ga Manzanni.

عُذْرًا أَوْ نُذْرًا ﴿٦﴾

Domin yanke hamzari ko dõmin gargadi.

إِنَّمَا تُوعَدُونَ لَوَٰقِعٌۭ ﴿٧﴾

Lalle ne, abin da ake yi muku wa'adi da shi tabbas mai aukuwa ne

فَإِذَا ٱلنُّجُومُ طُمِسَتْ ﴿٨﴾

To, idan taurãri aka shãfe haskensu.

وَإِذَا ٱلسَّمَآءُ فُرِجَتْ ﴿٩﴾

Kuma, idan sama aka tsãge ta.

وَإِذَا ٱلْجِبَالُ نُسِفَتْ ﴿١٠﴾

Kuma, idan duwãtsu aka nike su.

وَإِذَا ٱلرُّسُلُ أُقِّتَتْ ﴿١١﴾

Kuma, idan manzanni aka ƙayyade lõkacin tãra su.

لِأَىِّ يَوْمٍ أُجِّلَتْ ﴿١٢﴾

Domin babbar rãnar da aka yi wa ajali.

لِيَوْمِ ٱلْفَصْلِ ﴿١٣﴾

Domin rãnar rarrabẽwa.

وَمَآ أَدْرَىٰكَ مَا يَوْمُ ٱلْفَصْلِ ﴿١٤﴾

Kuma, me ya sanar da kai rãnar rarrabẽwa?

وَيْلٌۭ يَوْمَئِذٍۢ لِّلْمُكَذِّبِينَ ﴿١٥﴾

Bone yã tabbata a rãnar nan, ga mãsu ƙaryatãwa!

أَلَمْ نُهْلِكِ ٱلْأَوَّلِينَ ﴿١٦﴾

Ashe, ba Mu halakar da (mãsu ƙaryatãw) na farko ba.

ثُمَّ نُتْبِعُهُمُ ٱلْـَٔاخِرِينَ ﴿١٧﴾

Sa'an nan, kuma zã Mu biyar musu da na ƙarshe?

كَذَٰلِكَ نَفْعَلُ بِٱلْمُجْرِمِينَ ﴿١٨﴾

Haka nan, Muke aikatãwa da mãsu yin laifi.

وَيْلٌۭ يَوْمَئِذٍۢ لِّلْمُكَذِّبِينَ ﴿١٩﴾

Bone yã tabbata a rãnar nan ga mãsu ƙaryatãwa!

بسم الله الرحمن الرحيم Jum 24 Muharram
الجمعة 24 محرّم
هلال متناقص Gajimaren Raguwa Rana 25.1 / 29.5
Haske 20%
Wata Sabo a cikin kwana 4
لا إله إلا الله Babu abin bautawa sai Allah