الأعلى · Juz 30
Tafi zuwa
Alamomi
Mai karantawa / Qārī
Gudun sauti
Maimaita aya
Maimaita
Gungumewa kai
Fassara

Abubakar Mahmoud Gumi

Fontin larabci
Girman rubutu
Larabci
Fassara
Zangin da za a hadda
Maimaitawa
Kowane aya
Cikakken madauki
Babban mai karantawa
A ci gaba - Madauki A-B /

Kara Shafi 592 na Alkur'ani

Shafi 592 na Mushaf yana ɗauke da ayoyi 30. Yana cikin Juz 30, Hizb 60.

An sabunta a 10 Yuli 2026 03h52

Page 592 dans le Coran

30
ayoyi
30
Juz
60
Hizb
2
Surah
Juz 30
Shafi 592
سورة الأعلى
Juz 30 51.6% (291/564)
Hizb 60 5.2% (15/288)

بَلْ تُؤْثِرُونَ ٱلْحَيَوٰةَ ٱلدُّنْيَا ﴿١٦﴾

Ba haka ba! Kunã zãɓin rãyuwa ta kusa dũniya.

وَٱلْـَٔاخِرَةُ خَيْرٌۭ وَأَبْقَىٰٓ ﴿١٧﴾

Alhãli Lãhira ita ce mafi alheri kuma mafi wanzuwa.

إِنَّ هَـٰذَا لَفِى ٱلصُّحُفِ ٱلْأُولَىٰ ﴿١٨﴾

Lalle ne, wannan yanã a cikin littafan farko.

صُحُفِ إِبْرَٰهِيمَ وَمُوسَىٰ ﴿١٩﴾

Littaffan Ibrãhĩm da Mũsã.

هَلْ أَتَىٰكَ حَدِيثُ ٱلْغَـٰشِيَةِ ﴿١﴾

Lalle ne labãrin (¡iyãma) mai rufe mutãne da tsoronta yã zo maka?

وُجُوهٌۭ يَوْمَئِذٍ خَـٰشِعَةٌ ﴿٢﴾

Wasu huskõki a rãnar nan ƙasƙantattu ne.

عَامِلَةٌۭ نَّاصِبَةٌۭ ﴿٣﴾

Mãsu aikin wahala ne, mãsu gajiya.

تَصْلَىٰ نَارًا حَامِيَةًۭ ﴿٤﴾

Zã su shiga wata wuta mai zãfi.

تُسْقَىٰ مِنْ عَيْنٍ ءَانِيَةٍۢ ﴿٥﴾

Ana shãyar da su daga wani marmaro mai zãfin ruwa.

لَّيْسَ لَهُمْ طَعَامٌ إِلَّا مِن ضَرِيعٍۢ ﴿٦﴾

Ba su da wani abinci fãce dai daga danyi.

لَّا يُسْمِنُ وَلَا يُغْنِى مِن جُوعٍۢ ﴿٧﴾

Bã ya sanya ƙiba, kuma bã zai wadãtar daga yunwa ba.

وُجُوهٌۭ يَوْمَئِذٍۢ نَّاعِمَةٌۭ ﴿٨﴾

Wasu huskõki a rãnar nan mãsu ni'ima ne.

لِّسَعْيِهَا رَاضِيَةٌۭ ﴿٩﴾

Game da aikinsu, masu yarda ne.

فِى جَنَّةٍ عَالِيَةٍۢ ﴿١٠﴾

(Suna) a cikin Aljanna maɗaukakiya.

لَّا تَسْمَعُ فِيهَا لَـٰغِيَةًۭ ﴿١١﴾

Bã zã su ji yãsassar magana ba, a cikinta.

فِيهَا عَيْنٌۭ جَارِيَةٌۭ ﴿١٢﴾

A cikinta akwai marmaro mai gudãna.

فِيهَا سُرُرٌۭ مَّرْفُوعَةٌۭ ﴿١٣﴾

A cikinta akwai gadãje maɗaukaka.

وَأَكْوَابٌۭ مَّوْضُوعَةٌۭ ﴿١٤﴾

Da kõfuna ar'aje.

وَنَمَارِقُ مَصْفُوفَةٌۭ ﴿١٥﴾

Da filõli jẽre,

وَزَرَابِىُّ مَبْثُوثَةٌ ﴿١٦﴾

Da katifu shimfiɗe.

أَفَلَا يَنظُرُونَ إِلَى ٱلْإِبِلِ كَيْفَ خُلِقَتْ ﴿١٧﴾

Ashe to bã zã su dũbãwa ba ga rãƙumã yadda aka halitta su?

وَإِلَى ٱلسَّمَآءِ كَيْفَ رُفِعَتْ ﴿١٨﴾

Da zuwa ga sama yadda aka ɗaukaka ta?

وَإِلَى ٱلْجِبَالِ كَيْفَ نُصِبَتْ ﴿١٩﴾

Da zuwa ga duwãtsu yadda aka kafa su?

وَإِلَى ٱلْأَرْضِ كَيْفَ سُطِحَتْ ﴿٢٠﴾

Da zuwa ga ƙasa yadda aka shimfiɗã ta?

فَذَكِّرْ إِنَّمَآ أَنتَ مُذَكِّرٌۭ ﴿٢١﴾

sabõda haka, ka yi wa'azi, kai mai yin wa'azi ne kawai.

لَّسْتَ عَلَيْهِم بِمُصَيْطِرٍ ﴿٢٢﴾

Ba ka zama mai ĩkon tanƙwasãwa a kansu ba.

إِلَّا مَن تَوَلَّىٰ وَكَفَرَ ﴿٢٣﴾

Fãce dai duk wanda ya jũya bãya, kuma ya kãfirta.

فَيُعَذِّبُهُ ٱللَّهُ ٱلْعَذَابَ ٱلْأَكْبَرَ ﴿٢٤﴾

To, Allah zai yi masa azãba, azãbar nan da take mafi girma.

إِنَّ إِلَيْنَآ إِيَابَهُمْ ﴿٢٥﴾

Lalle ne, zuwa gare Mu kõmõwarsu take.

ثُمَّ إِنَّ عَلَيْنَا حِسَابَهُم ﴿٢٦﴾

Sa'an nan lalle ne aikinMu ne Mu yi musu hisãbi.

بسم الله الرحمن الرحيم Jum 24 Muharram
الجمعة 24 محرّم
هلال متناقص Gajimaren Raguwa Rana 25 / 29.5
Haske 21%
Wata Sabo a cikin kwana 4
لا إله إلا الله Babu abin bautawa sai Allah