العاديات · Juz 30
Tafi zuwa
Alamomi
Mai karantawa / Qārī
Gudun sauti
Maimaita aya
Maimaita
Gungumewa kai
Fassara

Abubakar Mahmoud Gumi

Fontin larabci
Girman rubutu
Larabci
Fassara
Zangin da za a hadda
Maimaitawa
Kowane aya
Cikakken madauki
Babban mai karantawa
A ci gaba - Madauki A-B /

Kara Shafi 600 na Alkur'ani

Shafi 600 na Mushaf yana ɗauke da ayoyi 21. Yana cikin Juz 30, Hizb 60.

An sabunta a 10 Yuli 2026 03h52

Page 600 dans le Coran

21
ayoyi
30
Juz
60
Hizb
3
Surah
Juz 30
Shafi 600
سورة العاديات
Juz 30 85.6% (483/564)
Hizb 60 71.9% (207/288)

وَحُصِّلَ مَا فِى ٱلصُّدُورِ ﴿١٠﴾

Aka bayyana abin da ke cikin zukata.

إِنَّ رَبَّهُم بِهِمْ يَوْمَئِذٍۢ لَّخَبِيرٌۢ ﴿١١﴾

Lalle ne Ubangijinsu, game da su a ranar nan Mai ƙididdigewa ne?

ٱلْقَارِعَةُ ﴿١﴾

Mai ƙwanƙwasar (zukata da tsõro)!

مَا ٱلْقَارِعَةُ ﴿٢﴾

Mẽnẽ ne mai ƙwanƙwasa?

وَمَآ أَدْرَىٰكَ مَا ٱلْقَارِعَةُ ﴿٣﴾

Kuma me ya sanar da kai abin da ake ce wa mai ƙwanƙwasa?

يَوْمَ يَكُونُ ٱلنَّاسُ كَٱلْفَرَاشِ ٱلْمَبْثُوثِ ﴿٤﴾

Rãnar da mutãne za su kasance kamar 'ya'yan fari mãsu wãtsuwa.

وَتَكُونُ ٱلْجِبَالُ كَٱلْعِهْنِ ٱلْمَنفُوشِ ﴿٥﴾

Kuma duwãtsu su kasance kamar gãshin sũfin da aka saɓe.

فَأَمَّا مَن ثَقُلَتْ مَوَٰزِينُهُۥ ﴿٦﴾

To, amma wanda ma'aunansa suka yi nauyi.

فَهُوَ فِى عِيشَةٍۢ رَّاضِيَةٍۢ ﴿٧﴾

To, shi yana a cikin wata rayuwa yardadda.

وَأَمَّا مَنْ خَفَّتْ مَوَٰزِينُهُۥ ﴿٨﴾

Kuma amma wanda ma'aunansa suka yi sauƙi (bãbu nauyi).

فَأُمُّهُۥ هَاوِيَةٌۭ ﴿٩﴾

To, uwarsa Hãwiya ce.

وَمَآ أَدْرَىٰكَ مَا هِيَهْ ﴿١٠﴾

Kuma me ya sanar da kai mece ce ita?

نَارٌ حَامِيَةٌۢ ﴿١١﴾

Wata wuta ce mai zafi.

أَلْهَىٰكُمُ ٱلتَّكَاثُرُ ﴿١﴾

Alfahari da yawan dũkiya da dangi ya shagaltar da ku (dagaibada mai amfaninku).

حَتَّىٰ زُرْتُمُ ٱلْمَقَابِرَ ﴿٢﴾

Har kuka ziyarci kaburbura.

كَلَّا سَوْفَ تَعْلَمُونَ ﴿٣﴾

A'aha! (Nan gaba) zã ku sani.

ثُمَّ كَلَّا سَوْفَ تَعْلَمُونَ ﴿٤﴾

Sa'an nan, tabbas, zã ku sani.

كَلَّا لَوْ تَعْلَمُونَ عِلْمَ ٱلْيَقِينِ ﴿٥﴾

Haƙĩƙa, da kuna da sani sani na yaƙĩni.

لَتَرَوُنَّ ٱلْجَحِيمَ ﴿٦﴾

Lalle ne da kuna ganin Jahĩm.

ثُمَّ لَتَرَوُنَّهَا عَيْنَ ٱلْيَقِينِ ﴿٧﴾

Sa'an nan lalle ne za ku gan ta, da idanu, bayyane.

ثُمَّ لَتُسْـَٔلُنَّ يَوْمَئِذٍ عَنِ ٱلنَّعِيمِ ﴿٨﴾

Sa'an nan lalle ne za a tambaye ku, a rãnar nan lãbãrin ni'imar (da aka yi muku).

بسم الله الرحمن الرحيم Jum 24 Muharram
الجمعة 24 محرّم
هلال متناقص Gajimaren Raguwa Rana 25.1 / 29.5
Haske 20%
Wata Sabo a cikin kwana 4
سبحان الله Subhanallah - Tsarkin Allah