البلد · Juz 30
Tafi zuwa
Alamomi
Mai karantawa / Qārī
Gudun sauti
Maimaita aya
Maimaita
Gungumewa kai
Fassara

Abubakar Mahmoud Gumi

Fontin larabci
Girman rubutu
Larabci
Fassara
Zangin da za a hadda
Maimaitawa
Kowane aya
Cikakken madauki
Babban mai karantawa
A ci gaba - Madauki A-B /

Kara Ruku'u 532 na Alkur'ani

Ruku'u 532 daga Surah Al-Balad ne (ayoyi 1 zuwa 20). Yana ɗauke da ayoyi 20 kuma yana cikin Juz 30.

An sabunta a 10 Yuli 2026 03h52

Ruku 532 dans le Coran

20
ayoyi
1
Surah
30
Juz
v.1 – v.20
Ayoyi

Sourate dans le Ruku 532

Shafi 594
Ruku'u 532
سورة الفجر
Juz 30 62.2% (351/564)
Hizb 60 26.0% (75/288)

لَآ أُقْسِمُ بِهَـٰذَا ٱلْبَلَدِ ﴿١﴾

Bã sai Na yi rantsuwa da wannan gari ba.

وَأَنتَ حِلٌّۢ بِهَـٰذَا ٱلْبَلَدِ ﴿٢﴾

Alhãli kai kanã mai sauka a cikin wannan gari.

وَوَالِدٍۢ وَمَا وَلَدَ ﴿٣﴾

Da mahaifi da abin da ya haifa.

لَقَدْ خَلَقْنَا ٱلْإِنسَـٰنَ فِى كَبَدٍ ﴿٤﴾

Lalle ne, Mun halitta mutum cikin wahala.

أَيَحْسَبُ أَن لَّن يَقْدِرَ عَلَيْهِ أَحَدٌۭ ﴿٥﴾

Kõ yanã zaton bãbu wani mai iya sãmun iko, a kansa?

يَقُولُ أَهْلَكْتُ مَالًۭا لُّبَدًا ﴿٦﴾

Yana cẽwa "Na halakarda dũkiya mai yawa,"

أَيَحْسَبُ أَن لَّمْ يَرَهُۥٓ أَحَدٌ ﴿٧﴾

Shin, yana zaton cewa wani bai gan shi ba?

أَلَمْ نَجْعَل لَّهُۥ عَيْنَيْنِ ﴿٨﴾

Shin, ba Mu sanya masa idãnu biyu ba?

وَلِسَانًۭا وَشَفَتَيْنِ ﴿٩﴾

Da harshe, da leɓɓa biyu.

وَهَدَيْنَـٰهُ ٱلنَّجْدَيْنِ ﴿١٠﴾

Kuma ba Mu shiryar da shi ga hanyõyi biyu ba?

فَلَا ٱقْتَحَمَ ٱلْعَقَبَةَ ﴿١١﴾

To, don mene ne bai shiga Aƙabã ba?

وَمَآ أَدْرَىٰكَ مَا ٱلْعَقَبَةُ ﴿١٢﴾

Kuma mene ne ya sanar da kai abin da ake cẽ wa Aƙabã?

فَكُّ رَقَبَةٍ ﴿١٣﴾

Ita ce fansar wuyan bãwa.

أَوْ إِطْعَـٰمٌۭ فِى يَوْمٍۢ ذِى مَسْغَبَةٍۢ ﴿١٤﴾

Ko kuwa ciyarwa, a cikin yini ma'abũcin yunwa.

يَتِيمًۭا ذَا مَقْرَبَةٍ ﴿١٥﴾

Ga marãya ma'abũcin zumunta.

أَوْ مِسْكِينًۭا ذَا مَتْرَبَةٍۢ ﴿١٦﴾

Ko kuwa wani matalauci ma'abũcin turɓãya.

ثُمَّ كَانَ مِنَ ٱلَّذِينَ ءَامَنُوا۟ وَتَوَاصَوْا۟ بِٱلصَّبْرِ وَتَوَاصَوْا۟ بِٱلْمَرْحَمَةِ ﴿١٧﴾

Sa'an nan kuma ya kasance daga waɗanda suka yi ĩmãni, kuma suka yi wa jũna wasiyya da yin haƙuri, kuma suka yi wa jũna wasiyya da tausayi.

أُو۟لَـٰٓئِكَ أَصْحَـٰبُ ٱلْمَيْمَنَةِ ﴿١٨﴾

Waɗannan ne ma'abũta albarka

وَٱلَّذِينَ كَفَرُوا۟ بِـَٔايَـٰتِنَا هُمْ أَصْحَـٰبُ ٱلْمَشْـَٔمَةِ ﴿١٩﴾

Kuma waɗanda suka kãfirta da ãyõyinMu, sũ ne ma'abũta shu'umci

عَلَيْهِمْ نَارٌۭ مُّؤْصَدَةٌۢ ﴿٢٠﴾

A kansu akwai wata wuta abar kullewa.

بسم الله الرحمن الرحيم Jum 24 Muharram
الجمعة 24 محرّم
هلال متناقص Gajimaren Raguwa Rana 25.1 / 29.5
Haske 21%
Wata Sabo a cikin kwana 4
لا حول ولا قوة إلا بالله Babu wata ƙarfi ko iko sai na Allah