Kara Shafi 532 na Alkur'ani

Shafi 532 na Mushaf yana ɗauke da ayoyi 24. Yana cikin Juz 27, Hizb 54.

An sabunta a 05 Agusta 2026 16h34

Shafi 532 a cikin Alkur'ani

24
ayoyi
27
Juz
54
Hizb
1
Surah

Surori a cikin Shafi 532

الرحمن · Juz 27
Juz 27
Shafi 532
سورة الرحمن
Juz 27 53.1% (212/399)
Hizb 54 7.9% (16/203)

رَبُّ ٱلْمَشْرِقَيْنِ وَرَبُّ ٱلْمَغْرِبَيْنِ ﴿١٧﴾

Ubangjin mafita biyu na rãnã, kuma Ubangijin mafãɗã biyu na rãnã.

فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ ﴿١٨﴾

To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

مَرَجَ ٱلْبَحْرَيْنِ يَلْتَقِيَانِ ﴿١٩﴾

Yã garwaya tẽku biyu (ruwan dãɗi da na zartsi) sunã haɗuwa.

بَيْنَهُمَا بَرْزَخٌۭ لَّا يَبْغِيَانِ ﴿٢٠﴾

A tsakãninsu akwai shãmaki, bã za su ƙetare haddi ba.

فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ ﴿٢١﴾

To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

يَخْرُجُ مِنْهُمَا ٱللُّؤْلُؤُ وَٱلْمَرْجَانُ ﴿٢٢﴾

Lu'ulu'u da murjãni na fita daga gare su.

فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ ﴿٢٣﴾

To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

وَلَهُ ٱلْجَوَارِ ٱلْمُنشَـَٔاتُ فِى ٱلْبَحْرِ كَٱلْأَعْلَـٰمِ ﴿٢٤﴾

Kuma Yanã da manyan jirãge, waɗanda ake ƙãgãwa a cikin tẽku kamar manyan duwãtsu.

فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ ﴿٢٥﴾

To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

كُلُّ مَنْ عَلَيْهَا فَانٍۢ ﴿٢٦﴾

Dukkan wanda ke kanta mai ƙãrẽwa ne.

وَيَبْقَىٰ وَجْهُ رَبِّكَ ذُو ٱلْجَلَـٰلِ وَٱلْإِكْرَامِ ﴿٢٧﴾

Kuma Fuskarar Ubangijinka, Mai girman Jalala da karimci, ita ce take wanzuwa.

فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ ﴿٢٨﴾

To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

يَسْـَٔلُهُۥ مَن فِى ٱلسَّمَـٰوَٰتِ وَٱلْأَرْضِ ۚ كُلَّ يَوْمٍ هُوَ فِى شَأْنٍۢ ﴿٢٩﴾

wanda ke a cikin sammai da ƙasã yanã rõƙon Sa (Allah), a kullum Allah na a cikin wani sha'ani.

فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ ﴿٣٠﴾

To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

سَنَفْرُغُ لَكُمْ أَيُّهَ ٱلثَّقَلَانِ ﴿٣١﴾

Zã mu ɗauki lõkaci sabõda ku, yã kũ mãsu nauyin halitta biyu!

فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ ﴿٣٢﴾

To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

يَـٰمَعْشَرَ ٱلْجِنِّ وَٱلْإِنسِ إِنِ ٱسْتَطَعْتُمْ أَن تَنفُذُوا۟ مِنْ أَقْطَارِ ٱلسَّمَـٰوَٰتِ وَٱلْأَرْضِ فَٱنفُذُوا۟ ۚ لَا تَنفُذُونَ إِلَّا بِسُلْطَـٰنٍۢ ﴿٣٣﴾

Ya jama'ar aljannu da mutãne! Idan kunã iya zarcẽwa daga sãsannin sammai da ƙasã to ku zarce. Bã za ku iya zarcẽwaba fãce da wani dalĩli.

فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ ﴿٣٤﴾

To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

يُرْسَلُ عَلَيْكُمَا شُوَاظٌۭ مِّن نَّارٍۢ وَنُحَاسٌۭ فَلَا تَنتَصِرَانِ ﴿٣٥﴾

Anã sako wani harshe daga wata wutã a kanku, da narkakkiyar tagulla. To, bã zã ku nẽmi taimako ba?

فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ ﴿٣٦﴾

To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

فَإِذَا ٱنشَقَّتِ ٱلسَّمَآءُ فَكَانَتْ وَرْدَةًۭ كَٱلدِّهَانِ ﴿٣٧﴾

Sa'an nan idan sama ta tsãge kuma ta zama jã kamar jar fãta.

فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ ﴿٣٨﴾

To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

فَيَوْمَئِذٍۢ لَّا يُسْـَٔلُ عَن ذَنۢبِهِۦٓ إِنسٌۭ وَلَا جَآنٌّۭ ﴿٣٩﴾

To, a ran nan bã zã a tambayi wani mutum laifinsa ba, kuma haka aljani.

فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ ﴿٤٠﴾

To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

بسم الله الرحمن الرحيم Lar 20 Safar
الأربعاء 20 صفر
أحدب متناقص Cikakken Wata Raguwa Rana 21.9 / 29.5
Haske 53%
Wata Sabo a cikin kwana 8
لا إله إلا الله Babu abin bautawa sai Allah