الرحمن · Juz 27
Tafi zuwa
Alamomi
Mai karantawa / Qārī
Gudun sauti
Maimaita aya
Maimaita
Gungumewa kai
Fassara

Abubakar Mahmoud Gumi

Fontin larabci
Girman rubutu
Larabci
Fassara
Zangin da za a hadda
Maimaitawa
Kowane aya
Cikakken madauki
Babban mai karantawa
A ci gaba - Madauki A-B /

Kara Surah Ar-Rahman

Surah Ar-Rahman (الرحمن) ita ce surah na Madina ta Alkur'ani tana da ayoyi 78. Ku karanta, ku saurari kuma ku hadda wannan surah tare da kayanmu masu hulɗa.

An sabunta a 10 Yuli 2026 03h52

📖 Karatu minti 4

Surah Ar-Rahman cikin lambobi

Tsarin saukarwa
Saukarwa n° 97 / 114
(na Madina)
354
kalmomi
-50.8% vs matsakaici
1,724
haruffa
-43.9% vs matsakaici
4
min karantawa
78
ayoyi
+42.6% vs matsakaici

Yawan amfani da kalmomin bincike في سورة Ar-Rahman

الله 0
رب 37

Babban jigo في سورة Ar-Rahman

#Rahman #Bienfaits #Création #Rétribution

Ayoyi masu muhimmanci في سورة Ar-Rahman

Maimaitawar aya: Répétition 31 fois

Shin kun sani? في سورة Ar-Rahman

Répète 31 fois 'Lequel donc des bienfaits de votre Seigneur nierez-vous?'

Haruffa da yawa suke fitowa في سورة Ar-Rahman

ا
218
#1
ن
142
#2
ل
138
#3
ب
124
#4
م
109
#5
Kara Surah Ar-Rahmaan
سورة الرحمن
Juz 27 53.1% (212/399)
Hizb 54 7.9% (16/203)

رَبُّ ٱلْمَشْرِقَيْنِ وَرَبُّ ٱلْمَغْرِبَيْنِ ﴿١٧﴾

Ubangjin mafita biyu na rãnã, kuma Ubangijin mafãɗã biyu na rãnã.

فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ ﴿١٨﴾

To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

مَرَجَ ٱلْبَحْرَيْنِ يَلْتَقِيَانِ ﴿١٩﴾

Yã garwaya tẽku biyu (ruwan dãɗi da na zartsi) sunã haɗuwa.

بَيْنَهُمَا بَرْزَخٌۭ لَّا يَبْغِيَانِ ﴿٢٠﴾

A tsakãninsu akwai shãmaki, bã za su ƙetare haddi ba.

فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ ﴿٢١﴾

To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

يَخْرُجُ مِنْهُمَا ٱللُّؤْلُؤُ وَٱلْمَرْجَانُ ﴿٢٢﴾

Lu'ulu'u da murjãni na fita daga gare su.

فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ ﴿٢٣﴾

To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

وَلَهُ ٱلْجَوَارِ ٱلْمُنشَـَٔاتُ فِى ٱلْبَحْرِ كَٱلْأَعْلَـٰمِ ﴿٢٤﴾

Kuma Yanã da manyan jirãge, waɗanda ake ƙãgãwa a cikin tẽku kamar manyan duwãtsu.

فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ ﴿٢٥﴾

To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

كُلُّ مَنْ عَلَيْهَا فَانٍۢ ﴿٢٦﴾

Dukkan wanda ke kanta mai ƙãrẽwa ne.

وَيَبْقَىٰ وَجْهُ رَبِّكَ ذُو ٱلْجَلَـٰلِ وَٱلْإِكْرَامِ ﴿٢٧﴾

Kuma Fuskarar Ubangijinka, Mai girman Jalala da karimci, ita ce take wanzuwa.

فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ ﴿٢٨﴾

To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

يَسْـَٔلُهُۥ مَن فِى ٱلسَّمَـٰوَٰتِ وَٱلْأَرْضِ ۚ كُلَّ يَوْمٍ هُوَ فِى شَأْنٍۢ ﴿٢٩﴾

wanda ke a cikin sammai da ƙasã yanã rõƙon Sa (Allah), a kullum Allah na a cikin wani sha'ani.

فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ ﴿٣٠﴾

To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

سَنَفْرُغُ لَكُمْ أَيُّهَ ٱلثَّقَلَانِ ﴿٣١﴾

Zã mu ɗauki lõkaci sabõda ku, yã kũ mãsu nauyin halitta biyu!

فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ ﴿٣٢﴾

To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

يَـٰمَعْشَرَ ٱلْجِنِّ وَٱلْإِنسِ إِنِ ٱسْتَطَعْتُمْ أَن تَنفُذُوا۟ مِنْ أَقْطَارِ ٱلسَّمَـٰوَٰتِ وَٱلْأَرْضِ فَٱنفُذُوا۟ ۚ لَا تَنفُذُونَ إِلَّا بِسُلْطَـٰنٍۢ ﴿٣٣﴾

Ya jama'ar aljannu da mutãne! Idan kunã iya zarcẽwa daga sãsannin sammai da ƙasã to ku zarce. Bã za ku iya zarcẽwaba fãce da wani dalĩli.

فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ ﴿٣٤﴾

To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

يُرْسَلُ عَلَيْكُمَا شُوَاظٌۭ مِّن نَّارٍۢ وَنُحَاسٌۭ فَلَا تَنتَصِرَانِ ﴿٣٥﴾

Anã sako wani harshe daga wata wutã a kanku, da narkakkiyar tagulla. To, bã zã ku nẽmi taimako ba?

فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ ﴿٣٦﴾

To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

فَإِذَا ٱنشَقَّتِ ٱلسَّمَآءُ فَكَانَتْ وَرْدَةًۭ كَٱلدِّهَانِ ﴿٣٧﴾

Sa'an nan idan sama ta tsãge kuma ta zama jã kamar jar fãta.

فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ ﴿٣٨﴾

To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

فَيَوْمَئِذٍۢ لَّا يُسْـَٔلُ عَن ذَنۢبِهِۦٓ إِنسٌۭ وَلَا جَآنٌّۭ ﴿٣٩﴾

To, a ran nan bã zã a tambayi wani mutum laifinsa ba, kuma haka aljani.

فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ ﴿٤٠﴾

To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

Kara Surah Ar-Rahmaan
سورة الرحمن
Juz 27 59.1% (236/399)
Hizb 54 19.7% (40/203)

يُعْرَفُ ٱلْمُجْرِمُونَ بِسِيمَـٰهُمْ فَيُؤْخَذُ بِٱلنَّوَٰصِى وَٱلْأَقْدَامِ ﴿٤١﴾

zã a iya sanin mãsu laifi da alãmarsu, sabõda haka sai a kãma kwarkaɗarsu da sãwãyensu.

فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ ﴿٤٢﴾

To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

هَـٰذِهِۦ جَهَنَّمُ ٱلَّتِى يُكَذِّبُ بِهَا ٱلْمُجْرِمُونَ ﴿٤٣﴾

Wannan Jahannama ce wadda mãsu laifi ke ƙaryatãwa game da ita.

يَطُوفُونَ بَيْنَهَا وَبَيْنَ حَمِيمٍ ءَانٍۢ ﴿٤٤﴾

Sunã kẽwaya a tsakaninta da ruwan ɗimi mai tsananin tafasa.

فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ ﴿٤٥﴾

To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

وَلِمَنْ خَافَ مَقَامَ رَبِّهِۦ جَنَّتَانِ ﴿٤٦﴾

Kuma wanda ya ji tsõron tsayãwa a gaba ga Ubangijinsa yanã da Aljanna biyu.

فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ ﴿٤٧﴾

To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

ذَوَاتَآ أَفْنَانٍۢ ﴿٤٨﴾

Mãsu rassan itãce.

فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ ﴿٤٩﴾

To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

فِيهِمَا عَيْنَانِ تَجْرِيَانِ ﴿٥٠﴾

A cikinsu akwai marẽmari biyu sunã gudãna.

فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ ﴿٥١﴾

To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

فِيهِمَا مِن كُلِّ فَـٰكِهَةٍۢ زَوْجَانِ ﴿٥٢﴾

A cikinsu akwai nau'i biyu daga kõwane 'ya'yan itãcen marmari.

فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ ﴿٥٣﴾

To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

مُتَّكِـِٔينَ عَلَىٰ فُرُشٍۭ بَطَآئِنُهَا مِنْ إِسْتَبْرَقٍۢ ۚ وَجَنَى ٱلْجَنَّتَيْنِ دَانٍۢ ﴿٥٤﴾

Sunã gincire a kan waɗansu shimfiɗu cikinsu tufãfin alharĩni mai kauri ne kuma nũnannun 'yã'yan itãcen Aljannar biyu kusakusa suke.

فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ ﴿٥٥﴾

To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

فِيهِنَّ قَـٰصِرَٰتُ ٱلطَّرْفِ لَمْ يَطْمِثْهُنَّ إِنسٌۭ قَبْلَهُمْ وَلَا جَآنٌّۭ ﴿٥٦﴾

A cikinsu akwai mãtã mãsu taƙaita ganinsu, wani mutum, gabanin mazajensu bai ɗebe budurcinsu ba kuma haka wani aljani.

فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ ﴿٥٧﴾

To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

كَأَنَّهُنَّ ٱلْيَاقُوتُ وَٱلْمَرْجَانُ ﴿٥٨﴾

Kamar dai su yaƙũtu ne da murjãni.

فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ ﴿٥٩﴾

To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

هَلْ جَزَآءُ ٱلْإِحْسَـٰنِ إِلَّا ٱلْإِحْسَـٰنُ ﴿٦٠﴾

Shin, kyautatãwa nã da wani sakamako? (Ã'aha) fãce kyautatãwa.

فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ ﴿٦١﴾

To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

وَمِن دُونِهِمَا جَنَّتَانِ ﴿٦٢﴾

Kuma baicinsu akwai waɗansu gidãjen Aljanna biyu.

فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ ﴿٦٣﴾

To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

مُدْهَآمَّتَانِ ﴿٦٤﴾

Mãsu duhun inuwa.

فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ ﴿٦٥﴾

To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

فِيهِمَا عَيْنَانِ نَضَّاخَتَانِ ﴿٦٦﴾

A cikinsu akwai marẽmari biyu masu kwarãrar ruwa.

فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ ﴿٦٧﴾

To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

Kara Surah Ar-Rahmaan
سورة الرحمن
Juz 27 65.9% (263/399)
Hizb 54 33.0% (67/203)

فِيهِمَا فَـٰكِهَةٌۭ وَنَخْلٌۭ وَرُمَّانٌۭ ﴿٦٨﴾

A cikinsu akwai 'ya'yan itãcen marmari da dabĩno darummãni.

فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ ﴿٦٩﴾

To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

فِيهِنَّ خَيْرَٰتٌ حِسَانٌۭ ﴿٧٠﴾

A cikinsu, akwai wasu mãtã mãsu kyaun hãlãye, mãsu kyaun halitta.

فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ ﴿٧١﴾

To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

حُورٌۭ مَّقْصُورَٰتٌۭ فِى ٱلْخِيَامِ ﴿٧٢﴾

Mãsu farin idãnu da baƙinsu waɗanda aka tsare a cikin haimõmi.

فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ ﴿٧٣﴾

To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

لَمْ يَطْمِثْهُنَّ إِنسٌۭ قَبْلَهُمْ وَلَا جَآنٌّۭ ﴿٧٤﴾

Wani mutum, gabanin mazajensu bai ɗẽbe budurcinsu ba, kuma haka wani aljani.

فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ ﴿٧٥﴾

To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

مُتَّكِـِٔينَ عَلَىٰ رَفْرَفٍ خُضْرٍۢ وَعَبْقَرِىٍّ حِسَانٍۢ ﴿٧٦﴾

Sunã gincire a kan wasu matãsai mãsu kõren launi da katĩfun Abkara kyãwãwa.

فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ ﴿٧٧﴾

To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

تَبَـٰرَكَ ٱسْمُ رَبِّكَ ذِى ٱلْجَلَـٰلِ وَٱلْإِكْرَامِ ﴿٧٨﴾

Sũnan Ubangjinka, Mai girman Jalãla da Karimci, ya tsarkaka.

بسم الله الرحمن الرحيم Jum 24 Muharram
الجمعة 24 محرّم
هلال متناقص Gajimaren Raguwa Rana 25 / 29.5
Haske 21%
Wata Sabo a cikin kwana 4
أستغفر الله Ina neman gafara daga Allah