Kara Shafi 575 na Alkur'ani

Shafi 575 na Mushaf yana ɗauke da ayoyi 18. Yana cikin Juz 29, Hizb 58.

An sabunta a 05 Agusta 2026 16h34

Shafi 575 a cikin Alkur'ani

18
ayoyi
29
Juz
58
Hizb
2
Surah
المزمل · Juz 29
Juz 29
Shafi 575
سورة المزمل
Juz 29 58.7% (253/431)
Hizb 58 20.9% (47/225)

۞ إِنَّ رَبَّكَ يَعْلَمُ أَنَّكَ تَقُومُ أَدْنَىٰ مِن ثُلُثَىِ ٱلَّيْلِ وَنِصْفَهُۥ وَثُلُثَهُۥ وَطَآئِفَةٌۭ مِّنَ ٱلَّذِينَ مَعَكَ ۚ وَٱللَّهُ يُقَدِّرُ ٱلَّيْلَ وَٱلنَّهَارَ ۚ عَلِمَ أَن لَّن تُحْصُوهُ فَتَابَ عَلَيْكُمْ ۖ فَٱقْرَءُوا۟ مَا تَيَسَّرَ مِنَ ٱلْقُرْءَانِ ۚ عَلِمَ أَن سَيَكُونُ مِنكُم مَّرْضَىٰ ۙ وَءَاخَرُونَ يَضْرِبُونَ فِى ٱلْأَرْضِ يَبْتَغُونَ مِن فَضْلِ ٱللَّهِ ۙ وَءَاخَرُونَ يُقَـٰتِلُونَ فِى سَبِيلِ ٱللَّهِ ۖ فَٱقْرَءُوا۟ مَا تَيَسَّرَ مِنْهُ ۚ وَأَقِيمُوا۟ ٱلصَّلَوٰةَ وَءَاتُوا۟ ٱلزَّكَوٰةَ وَأَقْرِضُوا۟ ٱللَّهَ قَرْضًا حَسَنًۭا ۚ وَمَا تُقَدِّمُوا۟ لِأَنفُسِكُم مِّنْ خَيْرٍۢ تَجِدُوهُ عِندَ ٱللَّهِ هُوَ خَيْرًۭا وَأَعْظَمَ أَجْرًۭا ۚ وَٱسْتَغْفِرُوا۟ ٱللَّهَ ۖ إِنَّ ٱللَّهَ غَفُورٌۭ رَّحِيمٌۢ ﴿٢٠﴾

Lalle ne, Ubangijinka Yã sani cẽwa, kai kana tsayuwa a kusan kashi biyu daga uku na dare, da rabinsa, da sulusinsa, tãre da wani ɓangare na waɗanda ke tãre da kai. Allah Yake iya ƙaddara dare da yini, Ya san bã zã ku iya lissafa shi ba, sabõda haka Ya karɓi tubarku sai, ku karanta abin da ya sauƙaƙa na Alƙur'ãni. Ya san wasu daga cikinku, zã su yi cĩwo, kuma wasu zã su yi tafiya cikin ƙasa suna nẽman falalar Allah da fatauci, kuma wasu zã su yi yãƙi a cikin banyar Allah. Sabõda haka ku karanta abin da ya sauƙaƙa daga gare shi, kuma ku tsai da salla kuma ku bãyar da zakka, kumaa ku bai wa Allah rance, rance mai kyãwo. Kuma abin da kuka gabatar dõmin kanku, na alhẽri, zã ku sãme shi a wurin Allah zai kasance mafifici (daga wanda kuka ajiye) kuma zai fi girma ga sakamako, kuma ku rõƙi Allah gãfara; lalle ne Allah Mai gãfara ne, Mai jin ƙai.

يَـٰٓأَيُّهَا ٱلْمُدَّثِّرُ ﴿١﴾

Yã wanda ya lulluɓa da mayãfi.

قُمْ فَأَنذِرْ ﴿٢﴾

Ka tãshi dõmin ka yi gargaɗi

وَرَبَّكَ فَكَبِّرْ ﴿٣﴾

Kuma Ubangijinka, sai ka girmama Shi,

وَثِيَابَكَ فَطَهِّرْ ﴿٤﴾

Kuma tutãfinka, sai ka tsarkake su,

وَٱلرُّجْزَ فَٱهْجُرْ ﴿٥﴾

Kuma gumãka, sai ka ƙaurace musu.

وَلَا تَمْنُن تَسْتَكْثِرُ ﴿٦﴾

Kada ka yi kyauta kana nẽman ƙãri

وَلِرَبِّكَ فَٱصْبِرْ ﴿٧﴾

Kuma sabõda Ubangijinka? Sai ka yi haƙure

فَإِذَا نُقِرَ فِى ٱلنَّاقُورِ ﴿٨﴾

To, idan aka yi bũsa a cikin ƙaho.

فَذَٰلِكَ يَوْمَئِذٍۢ يَوْمٌ عَسِيرٌ ﴿٩﴾

To, wannan, a rãnar nan, yini ne mai wuya

عَلَى ٱلْكَـٰفِرِينَ غَيْرُ يَسِيرٍۢ ﴿١٠﴾

A kan kãfirai, bã mai sauƙi ba ne.

ذَرْنِى وَمَنْ خَلَقْتُ وَحِيدًۭا ﴿١١﴾

Ka bar Ni da wanda Na halitta, yana shi kaɗai,

وَجَعَلْتُ لَهُۥ مَالًۭا مَّمْدُودًۭا ﴿١٢﴾

Kuma Na sanya masa dũkiya shimfiɗaɗɗiya

وَبَنِينَ شُهُودًۭا ﴿١٣﴾

Da ɗiyã halartattu,

وَمَهَّدتُّ لَهُۥ تَمْهِيدًۭا ﴿١٤﴾

Kuma Na shimfiɗa? masa kõme shimfiɗãwa.

ثُمَّ يَطْمَعُ أَنْ أَزِيدَ ﴿١٥﴾

Sa'an nan, yanã kwaɗayin in yi masa ƙãri!

كَلَّآ ۖ إِنَّهُۥ كَانَ لِـَٔايَـٰتِنَا عَنِيدًۭا ﴿١٦﴾

Faufau! Lalle ne, shĩ yã kasance, ga ãyõyinMu, mai tsaurin kai.

سَأُرْهِقُهُۥ صَعُودًا ﴿١٧﴾

Zã Ni kallafa masa wahala mai hauhawa.

بسم الله الرحمن الرحيم Lar 20 Safar
الأربعاء 20 صفر
أحدب متناقص Cikakken Wata Raguwa Rana 21.9 / 29.5
Haske 53%
Wata Sabo a cikin kwana 8
سبحان الله Subhanallah - Tsarkin Allah