Abubakar Mahmoud Gumi
Surah Al-Humaza (الهمزة) ita ce surah na Makka ta Alkur'ani tana da ayoyi 9. Ku karanta, ku saurari kuma ku hadda wannan surah tare da kayanmu masu hulɗa.
An sabunta a 10 Yuli 2026 03h52
📖 Karatu minti 1coran.read_full_page : Kara Surah Al-Humaza →
وَيْلٌۭ لِّكُلِّ هُمَزَةٍۢ لُّمَزَةٍ ﴿١﴾
Bone ya tabbata ga duk mai nune, mai zunɗe (mai raɗa).
ٱلَّذِى جَمَعَ مَالًۭا وَعَدَّدَهُۥ ﴿٢﴾
Wanda ya tara dũkiya, kuma ya mayar da ita abar tattalinsa.
يَحْسَبُ أَنَّ مَالَهُۥٓ أَخْلَدَهُۥ ﴿٣﴾
Yana zaton cẽwa dũkiyarsa za ta dawwamar da shi.
كَلَّا ۖ لَيُنۢبَذَنَّ فِى ٱلْحُطَمَةِ ﴿٤﴾
A'aha! Lalle ne zã a jẽfa shi a cikin Huɗama.
وَمَآ أَدْرَىٰكَ مَا ٱلْحُطَمَةُ ﴿٥﴾
Kuma me ya sanar da kai abin da ake ce wa Huɗama?
نَارُ ٱللَّهِ ٱلْمُوقَدَةُ ﴿٦﴾
Wutar Allah ce wadda ake hurawa.
ٱلَّتِى تَطَّلِعُ عَلَى ٱلْأَفْـِٔدَةِ ﴿٧﴾
Wadda take lẽƙãwa a kan zukata.
إِنَّهَا عَلَيْهِم مُّؤْصَدَةٌۭ ﴿٨﴾
Lalle ne ita abar kullẽwa cea kansu.
فِى عَمَدٍۢ مُّمَدَّدَةٍۭ ﴿٩﴾
A cikin wasu ginshiƙai mĩƙaƙƙu.