Abubakar Mahmoud Gumi
Surah Al-Balad (البلد) ita ce surah na Makka ta Alkur'ani tana da ayoyi 20. Ku karanta, ku saurari kuma ku hadda wannan surah tare da kayanmu masu hulɗa.
An sabunta a 10 Yuli 2026 03h52
📖 Karatu minti 1coran.read_full_page : Kara Surah Al-Balad →
لَآ أُقْسِمُ بِهَـٰذَا ٱلْبَلَدِ ﴿١﴾
Bã sai Na yi rantsuwa da wannan gari ba.
وَأَنتَ حِلٌّۢ بِهَـٰذَا ٱلْبَلَدِ ﴿٢﴾
Alhãli kai kanã mai sauka a cikin wannan gari.
وَوَالِدٍۢ وَمَا وَلَدَ ﴿٣﴾
Da mahaifi da abin da ya haifa.
لَقَدْ خَلَقْنَا ٱلْإِنسَـٰنَ فِى كَبَدٍ ﴿٤﴾
Lalle ne, Mun halitta mutum cikin wahala.
أَيَحْسَبُ أَن لَّن يَقْدِرَ عَلَيْهِ أَحَدٌۭ ﴿٥﴾
Kõ yanã zaton bãbu wani mai iya sãmun iko, a kansa?
يَقُولُ أَهْلَكْتُ مَالًۭا لُّبَدًا ﴿٦﴾
Yana cẽwa "Na halakarda dũkiya mai yawa,"
أَيَحْسَبُ أَن لَّمْ يَرَهُۥٓ أَحَدٌ ﴿٧﴾
Shin, yana zaton cewa wani bai gan shi ba?
أَلَمْ نَجْعَل لَّهُۥ عَيْنَيْنِ ﴿٨﴾
Shin, ba Mu sanya masa idãnu biyu ba?
وَلِسَانًۭا وَشَفَتَيْنِ ﴿٩﴾
Da harshe, da leɓɓa biyu.
وَهَدَيْنَـٰهُ ٱلنَّجْدَيْنِ ﴿١٠﴾
Kuma ba Mu shiryar da shi ga hanyõyi biyu ba?
فَلَا ٱقْتَحَمَ ٱلْعَقَبَةَ ﴿١١﴾
To, don mene ne bai shiga Aƙabã ba?
وَمَآ أَدْرَىٰكَ مَا ٱلْعَقَبَةُ ﴿١٢﴾
Kuma mene ne ya sanar da kai abin da ake cẽ wa Aƙabã?
فَكُّ رَقَبَةٍ ﴿١٣﴾
Ita ce fansar wuyan bãwa.
أَوْ إِطْعَـٰمٌۭ فِى يَوْمٍۢ ذِى مَسْغَبَةٍۢ ﴿١٤﴾
Ko kuwa ciyarwa, a cikin yini ma'abũcin yunwa.
يَتِيمًۭا ذَا مَقْرَبَةٍ ﴿١٥﴾
Ga marãya ma'abũcin zumunta.
أَوْ مِسْكِينًۭا ذَا مَتْرَبَةٍۢ ﴿١٦﴾
Ko kuwa wani matalauci ma'abũcin turɓãya.
ثُمَّ كَانَ مِنَ ٱلَّذِينَ ءَامَنُوا۟ وَتَوَاصَوْا۟ بِٱلصَّبْرِ وَتَوَاصَوْا۟ بِٱلْمَرْحَمَةِ ﴿١٧﴾
Sa'an nan kuma ya kasance daga waɗanda suka yi ĩmãni, kuma suka yi wa jũna wasiyya da yin haƙuri, kuma suka yi wa jũna wasiyya da tausayi.
أُو۟لَـٰٓئِكَ أَصْحَـٰبُ ٱلْمَيْمَنَةِ ﴿١٨﴾
Waɗannan ne ma'abũta albarka
وَٱلَّذِينَ كَفَرُوا۟ بِـَٔايَـٰتِنَا هُمْ أَصْحَـٰبُ ٱلْمَشْـَٔمَةِ ﴿١٩﴾
Kuma waɗanda suka kãfirta da ãyõyinMu, sũ ne ma'abũta shu'umci
عَلَيْهِمْ نَارٌۭ مُّؤْصَدَةٌۢ ﴿٢٠﴾
A kansu akwai wata wuta abar kullewa.