Abubakar Mahmoud Gumi
Shafi 452 na Mushaf yana ɗauke da ayoyi 29. Yana cikin Juz 23, Hizb 46.
An sabunta a 10 Yuli 2026 03h52
coran.read_full_page : Kara Shafi 452 na Alkur'ani →
مَا لَكُمْ كَيْفَ تَحْكُمُونَ ﴿١٥٤﴾
Mẽ ya same ku? Yãya kuke hukuntãwa (wannanhukunci)?
أَفَلَا تَذَكَّرُونَ ﴿١٥٥﴾
Shin, bã ku tunãni?
أَمْ لَكُمْ سُلْطَـٰنٌۭ مُّبِينٌۭ ﴿١٥٦﴾
Ko kuma kunã da wani dalĩli bayyananne ne?
فَأْتُوا۟ بِكِتَـٰبِكُمْ إِن كُنتُمْ صَـٰدِقِينَ ﴿١٥٧﴾
To, ku zo da littãfinku idan kun kasance mãsu gaskiya.
وَجَعَلُوا۟ بَيْنَهُۥ وَبَيْنَ ٱلْجِنَّةِ نَسَبًۭا ۚ وَلَقَدْ عَلِمَتِ ٱلْجِنَّةُ إِنَّهُمْ لَمُحْضَرُونَ ﴿١٥٨﴾
Kuma suka sanya nasaba a tsakãninSa da tsakãnin aljannu. Alhãli kuwa Lalle aljannu sun sani, "Lalle sũ, haƙĩƙa waɗanda ake halartarwa ne (a cikin wutã.)"
سُبْحَـٰنَ ٱللَّهِ عَمَّا يَصِفُونَ ﴿١٥٩﴾
Tsarki ya tabbata ga Allah daga abin da suke siffantãwa.
إِلَّا عِبَادَ ٱللَّهِ ٱلْمُخْلَصِينَ ﴿١٦٠﴾
Sai bãyin Allah waɗanda aka tsarkake.
فَإِنَّكُمْ وَمَا تَعْبُدُونَ ﴿١٦١﴾
To, lalle, ku da abin da kuke bautãwa,
مَآ أَنتُمْ عَلَيْهِ بِفَـٰتِنِينَ ﴿١٦٢﴾
Ba ku zama mãsu buwãya ba a gare Shi.
إِلَّا مَنْ هُوَ صَالِ ٱلْجَحِيمِ ﴿١٦٣﴾
Sai wanda yake mai shiga babbar wutã Jahĩm.
وَمَا مِنَّآ إِلَّا لَهُۥ مَقَامٌۭ مَّعْلُومٌۭ ﴿١٦٤﴾
"Kuma bãbu kõwa daga cikinmu, fãce yanã da matsayi sananne."
وَإِنَّا لَنَحْنُ ٱلصَّآفُّونَ ﴿١٦٥﴾
"Kuma lalle mu, haƙĩƙa, mũ ne mãsu yin sahu-sahu (dõmin ibãda)."
وَإِنَّا لَنَحْنُ ٱلْمُسَبِّحُونَ ﴿١٦٦﴾
"Kuma lalle mũ haƙĩƙa, mũ ne mãsu yin tasbĩhi."
وَإِن كَانُوا۟ لَيَقُولُونَ ﴿١٦٧﴾
Kuma lalle sũ, sun kasance sunã cẽwa,
لَوْ أَنَّ عِندَنَا ذِكْرًۭا مِّنَ ٱلْأَوَّلِينَ ﴿١٦٨﴾
"Dã lalle munã da wani littãfi irin na mutãnen farko."
لَكُنَّا عِبَادَ ٱللَّهِ ٱلْمُخْلَصِينَ ﴿١٦٩﴾
"Lalle dã mun kasance bãyin Allah waɗanda aka tsarkake."
فَكَفَرُوا۟ بِهِۦ ۖ فَسَوْفَ يَعْلَمُونَ ﴿١٧٠﴾
Sai suka kãfirta da shi. Sabõda haka zã su sani.
وَلَقَدْ سَبَقَتْ كَلِمَتُنَا لِعِبَادِنَا ٱلْمُرْسَلِينَ ﴿١٧١﴾
Kuma lalle, haƙĩƙa kalmarMu ta gabãta ga bãyinMu, Manzanni.
إِنَّهُمْ لَهُمُ ٱلْمَنصُورُونَ ﴿١٧٢﴾
Lalle sũ, haƙĩƙa, sũ ne waɗanda ake taimako.
وَإِنَّ جُندَنَا لَهُمُ ٱلْغَـٰلِبُونَ ﴿١٧٣﴾
Kuma lalle rundunarMu, haƙĩƙa, sũ ne marinjaya.
فَتَوَلَّ عَنْهُمْ حَتَّىٰ حِينٍۢ ﴿١٧٤﴾
Sabõda haka juya daga barinsu, har a wani lõkaci.
وَأَبْصِرْهُمْ فَسَوْفَ يُبْصِرُونَ ﴿١٧٥﴾
Ka nũna musu (gaskiya), da haka zã su dinga gani.
أَفَبِعَذَابِنَا يَسْتَعْجِلُونَ ﴿١٧٦﴾
Shin fa, da azabarMu suke nẽman gaggãwa?
فَإِذَا نَزَلَ بِسَاحَتِهِمْ فَسَآءَ صَبَاحُ ٱلْمُنذَرِينَ ﴿١٧٧﴾
To, idan ta sauka ga farfãjiyarsu, to, sãfiyar wadanda ake yi wa gargaɗi ta mũnana.
وَتَوَلَّ عَنْهُمْ حَتَّىٰ حِينٍۢ ﴿١٧٨﴾
Kuma ka jũya daga barinsu har a wani lõkaci.
وَأَبْصِرْ فَسَوْفَ يُبْصِرُونَ ﴿١٧٩﴾
Ka nũna (musu gaskiya), da haka zã su dinga nũnãwa.
سُبْحَـٰنَ رَبِّكَ رَبِّ ٱلْعِزَّةِ عَمَّا يَصِفُونَ ﴿١٨٠﴾
Tsarki ya tabbata ga Ubangijinka, Ubangijin rinjãye, daga barin abin da suke siffantãwa.
وَسَلَـٰمٌ عَلَى ٱلْمُرْسَلِينَ ﴿١٨١﴾
Kuma aminci ya tabbata ga Manzanni.
وَٱلْحَمْدُ لِلَّهِ رَبِّ ٱلْعَـٰلَمِينَ ﴿١٨٢﴾
Kuma gõdiya ta tabbata ga Allah Ubangijin halittu.