المدثر · Juz 29
Tafi zuwa
Alamomi
Mai karantawa / Qārī
Gudun sauti
Maimaita aya
Maimaita
Gungumewa kai
Fassara

Abubakar Mahmoud Gumi

Fontin larabci
Girman rubutu
Larabci
Fassara
Zangin da za a hadda
Maimaitawa
Kowane aya
Cikakken madauki
Babban mai karantawa
A ci gaba - Madauki A-B /

Kara Shafi 577 na Alkur'ani

Shafi 577 na Mushaf yana ɗauke da ayoyi 28. Yana cikin Juz 29, Hizb 58.

An sabunta a 10 Yuli 2026 03h52

Page 577 dans le Coran

28
ayoyi
29
Juz
58
Hizb
2
Surah
Juz 29
Shafi 577
سورة المدثر
Juz 29 69.8% (301/431)
Hizb 58 42.2% (95/225)

فَمَا تَنفَعُهُمْ شَفَـٰعَةُ ٱلشَّـٰفِعِينَ ﴿٤٨﴾

Sabõda haka cẽton mãsu cẽto bã zai amfãne su ba.

فَمَا لَهُمْ عَنِ ٱلتَّذْكِرَةِ مُعْرِضِينَ ﴿٤٩﴾

Haba! Me ya same su, suka zama mãsu bijirewa daga wa'azin gaskiya.

كَأَنَّهُمْ حُمُرٌۭ مُّسْتَنفِرَةٌۭ ﴿٥٠﴾

Kamar dai sũ, jãkuna firgitattu ne.

فَرَّتْ مِن قَسْوَرَةٍۭ ﴿٥١﴾

Sun gudu daga zãki.

بَلْ يُرِيدُ كُلُّ ٱمْرِئٍۢ مِّنْهُمْ أَن يُؤْتَىٰ صُحُفًۭا مُّنَشَّرَةًۭ ﴿٥٢﴾

A'aha! Kõwãne mutum daga cikinsu yanã son a zo masa da takardu (da sũnansa) ana wãtsãwa

كَلَّا ۖ بَل لَّا يَخَافُونَ ٱلْـَٔاخِرَةَ ﴿٥٣﴾

A'aha! Kai dai, bã su jin tsõron Lãhira.

كَلَّآ إِنَّهُۥ تَذْكِرَةٌۭ ﴿٥٤﴾

A'aha! Lalle ne, shi (Alƙur'ãni) tunãtarwa ce.

فَمَن شَآءَ ذَكَرَهُۥ ﴿٥٥﴾

Dõmin wanda ya so, ya tuna.

وَمَا يَذْكُرُونَ إِلَّآ أَن يَشَآءَ ٱللَّهُ ۚ هُوَ أَهْلُ ٱلتَّقْوَىٰ وَأَهْلُ ٱلْمَغْفِرَةِ ﴿٥٦﴾

Kuma bã zã su tuna ba fãce idan Allah Ya so, Shi ne Ya cancanta a bi Shi da taƙawa kuma Ya cancanta ga Ya yi gãfara.

لَآ أُقْسِمُ بِيَوْمِ ٱلْقِيَـٰمَةِ ﴿١﴾

Bã sai Nã yi rantsuwa da Rãnar ¡iyãma ba.

وَلَآ أُقْسِمُ بِٱلنَّفْسِ ٱللَّوَّامَةِ ﴿٢﴾

Bã sai Nã yi rantsuwa da rai mai yawan zargin kansa ba.

أَيَحْسَبُ ٱلْإِنسَـٰنُ أَلَّن نَّجْمَعَ عِظَامَهُۥ ﴿٣﴾

Sin, mutum yana zaton cẽwa bã zã Mu tãra ƙasusuwansa ba?

بَلَىٰ قَـٰدِرِينَ عَلَىٰٓ أَن نُّسَوِّىَ بَنَانَهُۥ ﴿٤﴾

Na'am! Mãsu ĩkon yi Muke a kan Mu daidaita gaɓõɓin yãtsunsa.

بَلْ يُرِيدُ ٱلْإِنسَـٰنُ لِيَفْجُرَ أَمَامَهُۥ ﴿٥﴾

Ba haka ba! Mutum so yake, ya yi fãjirci, ya ƙaryata abin da yake a gabansa.

يَسْـَٔلُ أَيَّانَ يَوْمُ ٱلْقِيَـٰمَةِ ﴿٦﴾

Yanã tambaya: "Yaushe ne Rãnar ¡iyãma?"

فَإِذَا بَرِقَ ٱلْبَصَرُ ﴿٧﴾

To, idan gani ya ɗimauta (ya yi ƙyalli).

وَخَسَفَ ٱلْقَمَرُ ﴿٨﴾

Kuma, watã ya yi husũfi (haskensa ya dushe).

وَجُمِعَ ٱلشَّمْسُ وَٱلْقَمَرُ ﴿٩﴾

Aka tãra rãnã da watã

يَقُولُ ٱلْإِنسَـٰنُ يَوْمَئِذٍ أَيْنَ ٱلْمَفَرُّ ﴿١٠﴾

Mutum zai ce a rãn nan "Ina wurin gudu?"

كَلَّا لَا وَزَرَ ﴿١١﴾

A'aha! bãbu mafaka.

إِلَىٰ رَبِّكَ يَوْمَئِذٍ ٱلْمُسْتَقَرُّ ﴿١٢﴾

zuwa ga Ubangijinka wurin tabbata, a rãnar nan, yake.

يُنَبَّؤُا۟ ٱلْإِنسَـٰنُ يَوْمَئِذٍۭ بِمَا قَدَّمَ وَأَخَّرَ ﴿١٣﴾

Ana gayã wa mutum, a rãnar nan, abin da ya gabatar da wanda ya jinkirtar.

بَلِ ٱلْإِنسَـٰنُ عَلَىٰ نَفْسِهِۦ بَصِيرَةٌۭ ﴿١٤﴾

Ba haka ba! Mutum, ga abin da ya shafi kansa, masani ne.

وَلَوْ أَلْقَىٰ مَعَاذِيرَهُۥ ﴿١٥﴾

Kuma ko da yã jẽfa uzurorinsa (bã zã a saurãre shi ba).

لَا تُحَرِّكْ بِهِۦ لِسَانَكَ لِتَعْجَلَ بِهِۦٓ ﴿١٦﴾

Kada ka mõtsar da harshenka game da shi dõmin ka yi gaugãwar riƙe shi (Alƙur'ãni).

إِنَّ عَلَيْنَا جَمْعَهُۥ وَقُرْءَانَهُۥ ﴿١٧﴾

Lalle ne, wãjibi ne a gare Mu, Mu tãra shi. Mu (tsare maka) karãtunsa.

فَإِذَا قَرَأْنَـٰهُ فَٱتَّبِعْ قُرْءَانَهُۥ ﴿١٨﴾

To idan Muka karanta shi sai ka bi karatunsa.

ثُمَّ إِنَّ عَلَيْنَا بَيَانَهُۥ ﴿١٩﴾

sa'an nan, lalle wãjibi ne a gare Mu, bayãninsa.

بسم الله الرحمن الرحيم Jum 24 Muharram
الجمعة 24 محرّم
هلال متناقص Gajimaren Raguwa Rana 25 / 29.5
Haske 21%
Wata Sabo a cikin kwana 4
سبحان الله وبحمده Tsarkin Allah da godiyarSa