النبإ · Juz 30
Tafi zuwa
Alamomi
Mai karantawa / Qārī
Gudun sauti
Maimaita aya
Maimaita
Gungumewa kai
Fassara

Abubakar Mahmoud Gumi

Fontin larabci
Girman rubutu
Larabci
Fassara
Zangin da za a hadda
Maimaitawa
Kowane aya
Cikakken madauki
Babban mai karantawa
A ci gaba - Madauki A-B /

Kara Shafi 583 na Alkur'ani

Shafi 583 na Mushaf yana ɗauke da ayoyi 25. Yana cikin Juz 30, Hizb 59.

An sabunta a 10 Yuli 2026 03h52

Page 583 dans le Coran

25
ayoyi
30
Juz
59
Hizb
2
Surah
Juz 30
Shafi 583
سورة النبإ
Juz 30 5.3% (30/564)
Hizb 59 10.9% (30/276)

إِنَّ لِلْمُتَّقِينَ مَفَازًا ﴿٣١﴾

Lalle ne, mãsu taƙawã nã da wani wurin sãmun babban rabo.

حَدَآئِقَ وَأَعْنَـٰبًۭا ﴿٣٢﴾

Lambuna da inabõbi.

وَكَوَاعِبَ أَتْرَابًۭا ﴿٣٣﴾

Da cikakkun 'yammata, tsãrar jũna.

وَكَأْسًۭا دِهَاقًۭا ﴿٣٤﴾

Da hinjãlan giya cikakku.

لَّا يَسْمَعُونَ فِيهَا لَغْوًۭا وَلَا كِذَّٰبًۭا ﴿٣٥﴾

Bã su jin yãsassar magana, a cikinta, kuma bã su jin ƙaryatãwa.

جَزَآءًۭ مِّن رَّبِّكَ عَطَآءً حِسَابًۭا ﴿٣٦﴾

Dõmin sakamako daga Ubangijinka, kyautã mai yawa.

رَّبِّ ٱلسَّمَـٰوَٰتِ وَٱلْأَرْضِ وَمَا بَيْنَهُمَا ٱلرَّحْمَـٰنِ ۖ لَا يَمْلِكُونَ مِنْهُ خِطَابًۭا ﴿٣٧﴾

Ubangijin sammai da ƙasa da abin da yake a tsakãninsu, Mai rahama, bã su da ikon yin wata magana daga gare Shi.

يَوْمَ يَقُومُ ٱلرُّوحُ وَٱلْمَلَـٰٓئِكَةُ صَفًّۭا ۖ لَّا يَتَكَلَّمُونَ إِلَّا مَنْ أَذِنَ لَهُ ٱلرَّحْمَـٰنُ وَقَالَ صَوَابًۭا ﴿٣٨﴾

Rãnar da Rũhi da malã'iku zã su tsaya a cikin safu, bã su magana, sai wanda Allah Ya yi masa izni, kuma ya faɗi abin da ke daidai.

ذَٰلِكَ ٱلْيَوْمُ ٱلْحَقُّ ۖ فَمَن شَآءَ ٱتَّخَذَ إِلَىٰ رَبِّهِۦ مَـَٔابًا ﴿٣٩﴾

Wancan, shi ne yini na gaskiya; to wanda ya so, ya riƙa makõma zuwa ga Ubangijinsa.

إِنَّآ أَنذَرْنَـٰكُمْ عَذَابًۭا قَرِيبًۭا يَوْمَ يَنظُرُ ٱلْمَرْءُ مَا قَدَّمَتْ يَدَاهُ وَيَقُولُ ٱلْكَافِرُ يَـٰلَيْتَنِى كُنتُ تُرَٰبًۢا ﴿٤٠﴾

Lalle ne, Mũ, Mun yi muku gargaɗin azãba makusanciya, rãnar da mutum ke dũbi zuwa ga abin da hannãyensa suka aikata, kuma kafiri ya ce: "Kaitona, dã dai nã zama turɓãya!"

وَٱلنَّـٰزِعَـٰتِ غَرْقًۭا ﴿١﴾

Ina rantsuwa da mala'iku mãsu fisgar rãyuka (na kafirai) da ƙarfi.

وَٱلنَّـٰشِطَـٰتِ نَشْطًۭا ﴿٢﴾

Da mãsu ɗibar rãyuka (na mũminai) da sauƙi a cikin nishãɗi.

وَٱلسَّـٰبِحَـٰتِ سَبْحًۭا ﴿٣﴾

Da mãsu sauka daga sama da umurnin Allah kamar suna iyo.

فَٱلسَّـٰبِقَـٰتِ سَبْقًۭا ﴿٤﴾

Sa'an nan, su zama mãsu gaugãwa (da umurnin Allah) kamar suna tsẽre.

فَٱلْمُدَبِّرَٰتِ أَمْرًۭا ﴿٥﴾

Sa, an nan, su kasance masu shirya gudanar da umurni.

يَوْمَ تَرْجُفُ ٱلرَّاجِفَةُ ﴿٦﴾

Rãnar da mai girgiza abũbuwa (bũsar farko) zã ta kaɗa.

تَتْبَعُهَا ٱلرَّادِفَةُ ﴿٧﴾

Mai biyar ta (bũsa ta biyu) nã biye.

قُلُوبٌۭ يَوْمَئِذٍۢ وَاجِفَةٌ ﴿٨﴾

Wasu zukãta, a rãnar nan, mãsu jin tsõro ne.

أَبْصَـٰرُهَا خَـٰشِعَةٌۭ ﴿٩﴾

Alhãli idãnunsu na ƙasƙantattu.

يَقُولُونَ أَءِنَّا لَمَرْدُودُونَ فِى ٱلْحَافِرَةِ ﴿١٠﴾

Sunã cẽwa "Ashe lalle zã a iya mayar da mu a kan sãwunmu?

أَءِذَا كُنَّا عِظَـٰمًۭا نَّخِرَةًۭ ﴿١١﴾

"Ashe, idan muka zama ƙasusuwa rududdugaggu?"

قَالُوا۟ تِلْكَ إِذًۭا كَرَّةٌ خَاسِرَةٌۭ ﴿١٢﴾

Suka ce: "Waccan kam kõmãwa ce, tãɓaɓɓiya!"

فَإِنَّمَا هِىَ زَجْرَةٌۭ وَٰحِدَةٌۭ ﴿١٣﴾

To, ita kam, tsãwa guda kawai ce.

فَإِذَا هُم بِٱلسَّاهِرَةِ ﴿١٤﴾

Sai kawai gã su a bãyan ƙasa.

هَلْ أَتَىٰكَ حَدِيثُ مُوسَىٰٓ ﴿١٥﴾

Shin, lãbãrin Mũsã ya zo maka?

بسم الله الرحمن الرحيم Jum 24 Muharram
الجمعة 24 محرّم
هلال متناقص Gajimaren Raguwa Rana 25 / 29.5
Haske 21%
Wata Sabo a cikin kwana 4
لا حول ولا قوة إلا بالله Babu wata ƙarfi ko iko sai na Allah