النازعات · Juz 30
Tafi zuwa
Alamomi
Mai karantawa / Qārī
Gudun sauti
Maimaita aya
Maimaita
Gungumewa kai
Fassara

Abubakar Mahmoud Gumi

Fontin larabci
Girman rubutu
Larabci
Fassara
Zangin da za a hadda
Maimaitawa
Kowane aya
Cikakken madauki
Babban mai karantawa
A ci gaba - Madauki A-B /

Kara Shafi 584 na Alkur'ani

Shafi 584 na Mushaf yana ɗauke da ayoyi 31. Yana cikin Juz 30, Hizb 59.

An sabunta a 10 Yuli 2026 03h52

Page 584 dans le Coran

31
ayoyi
30
Juz
59
Hizb
1
Surah

Sourate dans la page 584

Juz 30
Shafi 584
سورة النازعات
Juz 30 9.8% (55/564)
Hizb 59 19.9% (55/276)

إِذْ نَادَىٰهُ رَبُّهُۥ بِٱلْوَادِ ٱلْمُقَدَّسِ طُوًى ﴿١٦﴾

A lõkacin da Ubangijinsa Ya kirãye shi, a cikin kwari mai tsarki, wato Duwã?

ٱذْهَبْ إِلَىٰ فِرْعَوْنَ إِنَّهُۥ طَغَىٰ ﴿١٧﴾

Ka tafi zuwa ga Fir'auna, lalle ne shi, ya ƙẽtare haddi.

فَقُلْ هَل لَّكَ إِلَىٰٓ أَن تَزَكَّىٰ ﴿١٨﴾

"Sai ka ce masa, Kõ zã ka so ka tsarkaka.

وَأَهْدِيَكَ إِلَىٰ رَبِّكَ فَتَخْشَىٰ ﴿١٩﴾

"Kuma in shiryar da kai zuwa ga Ubangijinka domin ka ji tsoronSa?"

فَأَرَىٰهُ ٱلْـَٔايَةَ ٱلْكُبْرَىٰ ﴿٢٠﴾

Sai ya nũna masa ãyar nan mafi girma.

فَكَذَّبَ وَعَصَىٰ ﴿٢١﴾

Sai ya ƙaryata, kuma ya sãɓa (umurni),

ثُمَّ أَدْبَرَ يَسْعَىٰ ﴿٢٢﴾

Sa'an nan ya jũya bãya, yanã tafiya da sauri.

فَحَشَرَ فَنَادَىٰ ﴿٢٣﴾

Sai ya yi gayya, sa'an nan ya yi kira.

فَقَالَ أَنَا۠ رَبُّكُمُ ٱلْأَعْلَىٰ ﴿٢٤﴾

Sai ya ce: "Nĩ ne Ubangijinku mafi ɗaudaka."

فَأَخَذَهُ ٱللَّهُ نَكَالَ ٱلْـَٔاخِرَةِ وَٱلْأُولَىٰٓ ﴿٢٥﴾

Sabõda haka Allah Ya kama shi, dõmin azãbar maganar ƙarshe da ta farko.

إِنَّ فِى ذَٰلِكَ لَعِبْرَةًۭ لِّمَن يَخْشَىٰٓ ﴿٢٦﴾

Lalle ne, a cikin wannan haƙiƙa akwai abin kula ga wanda yake tsõron Allah.

ءَأَنتُمْ أَشَدُّ خَلْقًا أَمِ ٱلسَّمَآءُ ۚ بَنَىٰهَا ﴿٢٧﴾

Shin, kũ ne mafi wuyar halitta ko sama? Allah Ya gina ta.

رَفَعَ سَمْكَهَا فَسَوَّىٰهَا ﴿٢٨﴾

Ya ɗaukaka rufinta, sa'an nan Ya daidaita ta.

وَأَغْطَشَ لَيْلَهَا وَأَخْرَجَ ضُحَىٰهَا ﴿٢٩﴾

Kuma Ya duhuntar da darenta, kuma Ya fitar da hantsinta.

وَٱلْأَرْضَ بَعْدَ ذَٰلِكَ دَحَىٰهَآ ﴿٣٠﴾

Kuma, ƙasa a bayan haka Ya mulmula ta.

أَخْرَجَ مِنْهَا مَآءَهَا وَمَرْعَىٰهَا ﴿٣١﴾

Ya fitar da ruwanta daga gare ta da makiyãyarta.

وَٱلْجِبَالَ أَرْسَىٰهَا ﴿٣٢﴾

Da duwatsu, Yã kafe ta.

مَتَـٰعًۭا لَّكُمْ وَلِأَنْعَـٰمِكُمْ ﴿٣٣﴾

Domin jiyarwa dãɗi a gare ku, kuma ga dabbõbinku.

فَإِذَا جَآءَتِ ٱلطَّآمَّةُ ٱلْكُبْرَىٰ ﴿٣٤﴾

To, idan uwar masĩfu, mafi girma, ta zo.

يَوْمَ يَتَذَكَّرُ ٱلْإِنسَـٰنُ مَا سَعَىٰ ﴿٣٥﴾

Rãnar da mutum zai yi tunãnin abin da ya aikata.

وَبُرِّزَتِ ٱلْجَحِيمُ لِمَن يَرَىٰ ﴿٣٦﴾

Kuma, a bayyana Jahĩm ga mai gani.

فَأَمَّا مَن طَغَىٰ ﴿٣٧﴾

To, amma wanda ya yi girman kai.

وَءَاثَرَ ٱلْحَيَوٰةَ ٱلدُّنْيَا ﴿٣٨﴾

Kuma, ya zãɓi rãyuwa ta kusa, (wato dũniya).

فَإِنَّ ٱلْجَحِيمَ هِىَ ٱلْمَأْوَىٰ ﴿٣٩﴾

To, lalle ne Jahĩm, ita ce makõma.

وَأَمَّا مَنْ خَافَ مَقَامَ رَبِّهِۦ وَنَهَى ٱلنَّفْسَ عَنِ ٱلْهَوَىٰ ﴿٤٠﴾

Kuma, amma wanda ya ji tsõron tsayi a gaba ga Ubangijinsa, kuma ya kange kansa daga son rai.

فَإِنَّ ٱلْجَنَّةَ هِىَ ٱلْمَأْوَىٰ ﴿٤١﴾

To, lalle ne Aljanna ita ce makõma.

يَسْـَٔلُونَكَ عَنِ ٱلسَّاعَةِ أَيَّانَ مُرْسَىٰهَا ﴿٤٢﴾

Sunã tambayar ka game da sa'a, wai yaushe ne matabbatarta?

فِيمَ أَنتَ مِن ذِكْرَىٰهَآ ﴿٤٣﴾

Me ya haɗã ka da ambatonta?

إِلَىٰ رَبِّكَ مُنتَهَىٰهَآ ﴿٤٤﴾

Zuwa ga Ubangijinka ƙarshen al'amarinta yake.

إِنَّمَآ أَنتَ مُنذِرُ مَن يَخْشَىٰهَا ﴿٤٥﴾

Kai mai gargaɗi kawai ne ga mai tsõron ta.

كَأَنَّهُمْ يَوْمَ يَرَوْنَهَا لَمْ يَلْبَثُوٓا۟ إِلَّا عَشِيَّةً أَوْ ضُحَىٰهَا ﴿٤٦﴾

Kamar sũ a rãnar da zã su gan ta, ba su zauna ba fãce a lõkacin marẽce ko hantsinsa.

بسم الله الرحمن الرحيم Jum 24 Muharram
الجمعة 24 محرّم
هلال متناقص Gajimaren Raguwa Rana 25.1 / 29.5
Haske 21%
Wata Sabo a cikin kwana 4
الله أكبر Allah Shi ne Mafi Girma