Abubakar Mahmoud Gumi
Shafi 595 na Mushaf yana ɗauke da ayoyi 29. Yana cikin Juz 30, Hizb 60.
An sabunta a 10 Yuli 2026 03h52
coran.read_full_page : Kara Shafi 595 na Alkur'ani →
وَٱلشَّمْسِ وَضُحَىٰهَا ﴿١﴾
Ina rantsuwa da rãnã da hantsinta.
وَٱلْقَمَرِ إِذَا تَلَىٰهَا ﴿٢﴾
Kuma da wata idan ya bi ta.
وَٱلنَّهَارِ إِذَا جَلَّىٰهَا ﴿٣﴾
Da yini a lõkacin da ya bayyana ta.
وَٱلَّيْلِ إِذَا يَغْشَىٰهَا ﴿٤﴾
Da dare a lõkacin da ya ke rufe ta.
وَٱلسَّمَآءِ وَمَا بَنَىٰهَا ﴿٥﴾
Da sama da abin da ya gina ta.
وَٱلْأَرْضِ وَمَا طَحَىٰهَا ﴿٦﴾
Da ƙasã da abin da ya shimfiɗa ta.
وَنَفْسٍۢ وَمَا سَوَّىٰهَا ﴿٧﴾
Da rai da abin da ya daidaita shi.
فَأَلْهَمَهَا فُجُورَهَا وَتَقْوَىٰهَا ﴿٨﴾
Sa'an nan ya sanar da shi fãjircinsa da shiryuwarsa.
قَدْ أَفْلَحَ مَن زَكَّىٰهَا ﴿٩﴾
Lalle ne wanda ya tsarkake shi (rai) ya sãmi babban rabo.
وَقَدْ خَابَ مَن دَسَّىٰهَا ﴿١٠﴾
Kuma lalle ne wanda ya turbuɗe shi (da laifi) ya tãɓe.
كَذَّبَتْ ثَمُودُ بِطَغْوَىٰهَآ ﴿١١﴾
Samũdãwa sun ƙaryata (Annabinsu), dõmin girman kansu.
إِذِ ٱنۢبَعَثَ أَشْقَىٰهَا ﴿١٢﴾
A lõkacin da mafi shaƙãwarsu ya tafi (wurin sõke rãkumar sãlihu).
فَقَالَ لَهُمْ رَسُولُ ٱللَّهِ نَاقَةَ ٱللَّهِ وَسُقْيَـٰهَا ﴿١٣﴾
Sai Manzon Allah ya gaya musu cewa: "Ina tsõratar da ku ga rãƙumar Allah da ruwan shanta!"
فَكَذَّبُوهُ فَعَقَرُوهَا فَدَمْدَمَ عَلَيْهِمْ رَبُّهُم بِذَنۢبِهِمْ فَسَوَّىٰهَا ﴿١٤﴾
Sai suka ƙaryata shi, sa'an nan suka sõke ta. Sabõda haka Ubangijinsu Ya darkãke su, sabõda zunubinsu. Sa'an nan Ya daidaita ta (azãbar ga mai laifi da maras laifi).
وَلَا يَخَافُ عُقْبَـٰهَا ﴿١٥﴾
Kuma bã ya tsõron ãƙibarta (ita halakãwar).
وَٱلَّيْلِ إِذَا يَغْشَىٰ ﴿١﴾
Inã rantsuwa da dare a lõkacin da yake rufẽwa.
وَٱلنَّهَارِ إِذَا تَجَلَّىٰ ﴿٢﴾
Da yini a lõkacin da yake kuranyẽwa.
وَمَا خَلَقَ ٱلذَّكَرَ وَٱلْأُنثَىٰٓ ﴿٣﴾
Da abin da ya halitta namiji da mace.
إِنَّ سَعْيَكُمْ لَشَتَّىٰ ﴿٤﴾
Lãlle ne ayyukanku, dabam-dabam suke.
فَأَمَّا مَنْ أَعْطَىٰ وَٱتَّقَىٰ ﴿٥﴾
To, amma wanda ya yi kyauta, kuma ya yi taƙawa.
وَصَدَّقَ بِٱلْحُسْنَىٰ ﴿٦﴾
Kuma ya gaskata kalma mai kyãwo.
فَسَنُيَسِّرُهُۥ لِلْيُسْرَىٰ ﴿٧﴾
To, zã Mu sauƙaƙe masa har ya kai ga sauƙi.
وَأَمَّا مَنۢ بَخِلَ وَٱسْتَغْنَىٰ ﴿٨﴾
Kuma amma wanda ya yi rõwa, kuma ya wadãtu da kansa.
وَكَذَّبَ بِٱلْحُسْنَىٰ ﴿٩﴾
Kuma ya ƙaryatar da kalma mai kyãwo.
فَسَنُيَسِّرُهُۥ لِلْعُسْرَىٰ ﴿١٠﴾
To, zã Mu sauƙaƙke masa har ya kai ga tsanani.
وَمَا يُغْنِى عَنْهُ مَالُهُۥٓ إِذَا تَرَدَّىٰٓ ﴿١١﴾
Kuma dũkiyarsa ba ta wadãtar masa da kõme ba, a lõkacin da ya gangara (a wuta).
إِنَّ عَلَيْنَا لَلْهُدَىٰ ﴿١٢﴾
Lãlle aikinMu ne, Mu bayyana shiriya.
وَإِنَّ لَنَا لَلْـَٔاخِرَةَ وَٱلْأُولَىٰ ﴿١٣﴾
Kuma lalle ne Lãhira da duniya Namu ne.
فَأَنذَرْتُكُمْ نَارًۭا تَلَظَّىٰ ﴿١٤﴾
Sabõda haka, Na yi maku gargaɗi da wuta mai babbaka.