Kara Ruku'u 319 na Alkur'ani

Ruku'u 319 daga Surah Ash-Shuara ne (ayoyi 53 zuwa 69). Yana ɗauke da ayoyi 17 kuma yana cikin Juz 19.

An sabunta a 05 Agusta 2026 16h34

Ruku 319 a cikin Alkur'ani

17
ayoyi
1
Surah
19
Juz
v.53 – v.69
Ayoyi

Surori a cikin Ruku 319

الشعراء · Juz 19
Shafi 369
Ruku'u 319
سورة الشعراء
Juz 19 32.2% (109/339)
Hizb 37 65.3% (109/167)

فَأَرْسَلَ فِرْعَوْنُ فِى ٱلْمَدَآئِنِ حَـٰشِرِينَ ﴿٥٣﴾

Sai Fir'auna ya aika mãsu gayya a cikin birãne.

إِنَّ هَـٰٓؤُلَآءِ لَشِرْذِمَةٌۭ قَلِيلُونَ ﴿٥٤﴾

"Lalle ne, waɗannan, haƙĩƙa, ƙungiya ce kaɗan."

وَإِنَّهُمْ لَنَا لَغَآئِظُونَ ﴿٥٥﴾

"Kuma lalle ne sũ, a gare Mu, Mãsu fusãtarwa ne."

وَإِنَّا لَجَمِيعٌ حَـٰذِرُونَ ﴿٥٦﴾

"Kuma lalle ne mũ haƙĩƙa gabã ɗaya mãsu sauna ne."

فَأَخْرَجْنَـٰهُم مِّن جَنَّـٰتٍۢ وَعُيُونٍۢ ﴿٥٧﴾

Sai Muka fitar da su daga gonaki da marẽmari.

وَكُنُوزٍۢ وَمَقَامٍۢ كَرِيمٍۢ ﴿٥٨﴾

Da taskõki da mazauni mai kyau.

كَذَٰلِكَ وَأَوْرَثْنَـٰهَا بَنِىٓ إِسْرَٰٓءِيلَ ﴿٥٩﴾

Kamar haka! Kuma Muka gãdar da su ga Banĩ Isrãĩla.

فَأَتْبَعُوهُم مُّشْرِقِينَ ﴿٦٠﴾

Sai suka bĩ su sunã mãsu fita a lõkacin hũdõwar rãnã.

فَلَمَّا تَرَٰٓءَا ٱلْجَمْعَانِ قَالَ أَصْحَـٰبُ مُوسَىٰٓ إِنَّا لَمُدْرَكُونَ ﴿٦١﴾

Sa'an nan a lõkacin da jama'a biyu suka ga jũna, sai abõkan Mũsã suka ce: "Lalle ne mũ haƙĩ ƙa, waɗanda ake riska ne."

قَالَ كَلَّآ ۖ إِنَّ مَعِىَ رَبِّى سَيَهْدِينِ ﴿٦٢﴾

Ya ce: "Kayya! Lalle ne Ubangijina Yanã tare da ni, zai shiryar da ni."

فَأَوْحَيْنَآ إِلَىٰ مُوسَىٰٓ أَنِ ٱضْرِب بِّعَصَاكَ ٱلْبَحْرَ ۖ فَٱنفَلَقَ فَكَانَ كُلُّ فِرْقٍۢ كَٱلطَّوْدِ ٱلْعَظِيمِ ﴿٦٣﴾

Sai Muka yi wahayi zuwa ga Mũsã cẽwa "Ka dõki tẽku da sandarka." Sai tẽku ta tsãge, kõwane tsãgi ya kasance kamar falalen dũtse mai girma.

وَأَزْلَفْنَا ثَمَّ ٱلْـَٔاخَرِينَ ﴿٦٤﴾

Kuma Muka kusantar da waɗansu mutãne a can.

وَأَنجَيْنَا مُوسَىٰ وَمَن مَّعَهُۥٓ أَجْمَعِينَ ﴿٦٥﴾

Kuma Muka tsĩrar da Mũsã da waɗanda suke tãre da shi gabã ɗaya.

ثُمَّ أَغْرَقْنَا ٱلْـَٔاخَرِينَ ﴿٦٦﴾

Sa'an nan kuma Muka nutsar da waɗansu mutãnen.

إِنَّ فِى ذَٰلِكَ لَـَٔايَةًۭ ۖ وَمَا كَانَ أَكْثَرُهُم مُّؤْمِنِينَ ﴿٦٧﴾

Lalle ne a cikin wannan akwai ãyã, kuma mafi yawansu ba su kasance mãsu ĩmãni ba.

وَإِنَّ رَبَّكَ لَهُوَ ٱلْعَزِيزُ ٱلرَّحِيمُ ﴿٦٨﴾

Kuma lalle ne Ubangijinka, kaƙĩƙa, Shĩ ne Mabũwayi, Mai jin ƙai.

وَٱتْلُ عَلَيْهِمْ نَبَأَ إِبْرَٰهِيمَ ﴿٦٩﴾

Kuma ka karanta, a kansu, lãbãrin Ibrãhĩm.

بسم الله الرحمن الرحيم Lit 10 Rabi' al-Awwal
الاثنين 10 ربيع الأول
أحدب متزايد Cikakken Wata Tasowa Rana 11.3 / 29.5
Haske 87%
Cikakken Wata a cikin kwana 4
اللهم صل على محمد Ya Allah, ka saukar da tsira a kan Muhammad