الشعراء · Juz 19
Tafi zuwa
Alamomi
Mai karantawa / Qārī
Gudun sauti
Maimaita aya
Maimaita
Gungumewa kai
Fassara

Abubakar Mahmoud Gumi

Fontin larabci
Girman rubutu
Larabci
Fassara
Zangin da za a hadda
Maimaitawa
Kowane aya
Cikakken madauki
Babban mai karantawa
A ci gaba - Madauki A-B /

Kara Ruku'u 320 na Alkur'ani

Ruku'u 320 daga Surah Ash-Shuara ne (ayoyi 70 zuwa 104). Yana ɗauke da ayoyi 35 kuma yana cikin Juz 19.

An sabunta a 10 Yuli 2026 03h52

Ruku 320 dans le Coran

35
ayoyi
1
Surah
19
Juz
v.70 – v.104
Ayoyi

Sourate dans le Ruku 320

Shafi 371
Ruku'u 320
سورة الشعراء
Juz 19 41.3% (140/339)
Hizb 37 83.8% (140/167)

وَٱجْعَل لِّى لِسَانَ صِدْقٍۢ فِى ٱلْـَٔاخِرِينَ ﴿٨٤﴾

"Kuma Ka sanya mini harshen gaskiya a cikin mutãnen ƙarshe."

وَٱجْعَلْنِى مِن وَرَثَةِ جَنَّةِ ٱلنَّعِيمِ ﴿٨٥﴾

"Kuma Ka sanya ni daga magãdan Aljannar ni'ima."

وَٱغْفِرْ لِأَبِىٓ إِنَّهُۥ كَانَ مِنَ ٱلضَّآلِّينَ ﴿٨٦﴾

"Kuma Ka gãfarta wa ubãna, lalle ne shi, ya kasance daga ɓatattu."

وَلَا تُخْزِنِى يَوْمَ يُبْعَثُونَ ﴿٨٧﴾

"Kuma kada Ka kunyata ni a rãnar da ake tãyar da su."

يَوْمَ لَا يَنفَعُ مَالٌۭ وَلَا بَنُونَ ﴿٨٨﴾

"A rãnar da dũkiya bã ta amfãni, kuma ɗiya bã su yi."

إِلَّا مَنْ أَتَى ٱللَّهَ بِقَلْبٍۢ سَلِيمٍۢ ﴿٨٩﴾

"Fãce wanda ya jẽ wa Allah da zũciya mai tsarki."

وَأُزْلِفَتِ ٱلْجَنَّةُ لِلْمُتَّقِينَ ﴿٩٠﴾

Kuma aka kusantar da Aljanna ga mãsu taƙawa.

وَبُرِّزَتِ ٱلْجَحِيمُ لِلْغَاوِينَ ﴿٩١﴾

Kuma aka fitar da wutã babba dõmin halakakku.

وَقِيلَ لَهُمْ أَيْنَ مَا كُنتُمْ تَعْبُدُونَ ﴿٩٢﴾

Kuma aka ce musu, "Inã abin da kuka kasance kunã bautawa?"

مِن دُونِ ٱللَّهِ هَلْ يَنصُرُونَكُمْ أَوْ يَنتَصِرُونَ ﴿٩٣﴾

"Baicin Allah? Shin sunã tamakon ku kõ kuwa sunã tsare kansu?"

فَكُبْكِبُوا۟ فِيهَا هُمْ وَٱلْغَاوُۥنَ ﴿٩٤﴾

Sai aka kikkife su a cikinta, su da halakakkun.

وَجُنُودُ إِبْلِيسَ أَجْمَعُونَ ﴿٩٥﴾

Da rundunar Ibilĩsa gabã ɗaya.

قَالُوا۟ وَهُمْ فِيهَا يَخْتَصِمُونَ ﴿٩٦﴾

Suka ce: alhãli sunã a cikinta sunã yin husũma,

تَٱللَّهِ إِن كُنَّا لَفِى ضَلَـٰلٍۢ مُّبِينٍ ﴿٩٧﴾

"Rantsuwa da Allah! Lalle ne mun kasance, haƙĩƙa, a cikin ɓata bayyananna."

إِذْ نُسَوِّيكُم بِرَبِّ ٱلْعَـٰلَمِينَ ﴿٩٨﴾

"A lõkacin da muke daidaita ku da Ubangijin halittu.

وَمَآ أَضَلَّنَآ إِلَّا ٱلْمُجْرِمُونَ ﴿٩٩﴾

"Kuma bãbu abin da ya ɓatar da mu fãce mãsu laifi."

فَمَا لَنَا مِن شَـٰفِعِينَ ﴿١٠٠﴾

"Sabõda haka bã mu da waɗansu macẽta."

وَلَا صَدِيقٍ حَمِيمٍۢ ﴿١٠١﴾

"Kuma bã mu da abõki, masõyi."

فَلَوْ أَنَّ لَنَا كَرَّةًۭ فَنَكُونَ مِنَ ٱلْمُؤْمِنِينَ ﴿١٠٢﴾

"Sabõda haka dã lalle munã da (dãmar) kõmawa, dõmin mu kasance daga mũminai!"

إِنَّ فِى ذَٰلِكَ لَـَٔايَةًۭ ۖ وَمَا كَانَ أَكْثَرُهُم مُّؤْمِنِينَ ﴿١٠٣﴾

Lalle ne, a cikin wancan akwai ãyã, kuma mafi yawansu, bã su kasance mũminai ba.

وَإِنَّ رَبَّكَ لَهُوَ ٱلْعَزِيزُ ٱلرَّحِيمُ ﴿١٠٤﴾

Kuma lalle ne, Ubangijinka, Shi ne Mabuwãyi, Mai jin ƙai.

بسم الله الرحمن الرحيم Jum 24 Muharram
الجمعة 24 محرّم
هلال متناقص Gajimaren Raguwa Rana 25 / 29.5
Haske 21%
Wata Sabo a cikin kwana 4
حسبنا الله ونعم الوكيل Allah Ya isa mana, Shi ne mafi kyawun Mai Kiyaye