Abubakar Mahmoud Gumi
Ruku'u 466 daga Surah Ar-Rahman ne (ayoyi 1 zuwa 25). Yana ɗauke da ayoyi 25 kuma yana cikin Juz 27.
An sabunta a 10 Yuli 2026 03h52
coran.read_full_page : Kara Ruku'u 466 na Alkur'ani →
رَبُّ ٱلْمَشْرِقَيْنِ وَرَبُّ ٱلْمَغْرِبَيْنِ ﴿١٧﴾
Ubangjin mafita biyu na rãnã, kuma Ubangijin mafãɗã biyu na rãnã.
فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ ﴿١٨﴾
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
مَرَجَ ٱلْبَحْرَيْنِ يَلْتَقِيَانِ ﴿١٩﴾
Yã garwaya tẽku biyu (ruwan dãɗi da na zartsi) sunã haɗuwa.
بَيْنَهُمَا بَرْزَخٌۭ لَّا يَبْغِيَانِ ﴿٢٠﴾
A tsakãninsu akwai shãmaki, bã za su ƙetare haddi ba.
فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ ﴿٢١﴾
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
يَخْرُجُ مِنْهُمَا ٱللُّؤْلُؤُ وَٱلْمَرْجَانُ ﴿٢٢﴾
Lu'ulu'u da murjãni na fita daga gare su.
فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ ﴿٢٣﴾
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
وَلَهُ ٱلْجَوَارِ ٱلْمُنشَـَٔاتُ فِى ٱلْبَحْرِ كَٱلْأَعْلَـٰمِ ﴿٢٤﴾
Kuma Yanã da manyan jirãge, waɗanda ake ƙãgãwa a cikin tẽku kamar manyan duwãtsu.
فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ ﴿٢٥﴾
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?