Ruku'u 466 daga Surah Ar-Rahman ne (ayoyi 1 zuwa 25). Yana ɗauke da ayoyi 25 kuma yana cikin Juz 27.
An sabunta a 05 Agusta 2026 16h34
Karanta duka cikakken : Kara Ruku'u 466 na Alkur'ani →
ٱلرَّحْمَـٰنُ ﴿١﴾
(Allah) Mai rahama.
عَلَّمَ ٱلْقُرْءَانَ ﴿٢﴾
Yã sanar da Alƙur'ani.
خَلَقَ ٱلْإِنسَـٰنَ ﴿٣﴾
Yã halitta mutum.
عَلَّمَهُ ٱلْبَيَانَ ﴿٤﴾
Yã sanar da shi bayãni (magana).
ٱلشَّمْسُ وَٱلْقَمَرُ بِحُسْبَانٍۢ ﴿٥﴾
Rãnã da watã a kan lissãfi suke.
وَٱلنَّجْمُ وَٱلشَّجَرُ يَسْجُدَانِ ﴿٦﴾
Kuma tsirrai mãsu yãɗo da itãce sunã tawãlu'i.
وَٱلسَّمَآءَ رَفَعَهَا وَوَضَعَ ٱلْمِيزَانَ ﴿٧﴾
Kuma samã Ya ɗaukaka ta, Kuma Yã aza sikẽli.
أَلَّا تَطْغَوْا۟ فِى ٱلْمِيزَانِ ﴿٨﴾
Dõmin kada ku karkatar da sikẽlin.
وَأَقِيمُوا۟ ٱلْوَزْنَ بِٱلْقِسْطِ وَلَا تُخْسِرُوا۟ ٱلْمِيزَانَ ﴿٩﴾
Kuma ku daidaita awo da ãdalci, kuma kada ku rage sikẽlin.
وَٱلْأَرْضَ وَضَعَهَا لِلْأَنَامِ ﴿١٠﴾
Kuma ƙasã Yã aza ta dõmin tãlikai.
فِيهَا فَـٰكِهَةٌۭ وَٱلنَّخْلُ ذَاتُ ٱلْأَكْمَامِ ﴿١١﴾
A cikinta akwai 'ya'yan itãcen marmari da dabĩno mai kwasfa.
وَٱلْحَبُّ ذُو ٱلْعَصْفِ وَٱلرَّيْحَانُ ﴿١٢﴾
Da ƙwãya mai sõshiya da ƙamshi.
فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ ﴿١٣﴾
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangjinku kuke ƙaryatãwa?
خَلَقَ ٱلْإِنسَـٰنَ مِن صَلْصَـٰلٍۢ كَٱلْفَخَّارِ ﴿١٤﴾
Yã halitta mutum daga ƙẽkasasshen yumɓu kumar kasko.
وَخَلَقَ ٱلْجَآنَّ مِن مَّارِجٍۢ مِّن نَّارٍۢ ﴿١٥﴾
Kuma ya halitta aljani daga bira daga wutã.
فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ ﴿١٦﴾
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
رَبُّ ٱلْمَشْرِقَيْنِ وَرَبُّ ٱلْمَغْرِبَيْنِ ﴿١٧﴾
Ubangjin mafita biyu na rãnã, kuma Ubangijin mafãɗã biyu na rãnã.
فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ ﴿١٨﴾
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
مَرَجَ ٱلْبَحْرَيْنِ يَلْتَقِيَانِ ﴿١٩﴾
Yã garwaya tẽku biyu (ruwan dãɗi da na zartsi) sunã haɗuwa.
بَيْنَهُمَا بَرْزَخٌۭ لَّا يَبْغِيَانِ ﴿٢٠﴾
A tsakãninsu akwai shãmaki, bã za su ƙetare haddi ba.
فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ ﴿٢١﴾
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
يَخْرُجُ مِنْهُمَا ٱللُّؤْلُؤُ وَٱلْمَرْجَانُ ﴿٢٢﴾
Lu'ulu'u da murjãni na fita daga gare su.
فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ ﴿٢٣﴾
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
وَلَهُ ٱلْجَوَارِ ٱلْمُنشَـَٔاتُ فِى ٱلْبَحْرِ كَٱلْأَعْلَـٰمِ ﴿٢٤﴾
Kuma Yanã da manyan jirãge, waɗanda ake ƙãgãwa a cikin tẽku kamar manyan duwãtsu.
فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ ﴿٢٥﴾
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?