الواقعة · Juz 27
Tafi zuwa
Alamomi
Mai karantawa / Qārī
Gudun sauti
Maimaita aya
Maimaita
Gungumewa kai
Fassara

Abubakar Mahmoud Gumi

Fontin larabci
Girman rubutu
Larabci
Fassara
Zangin da za a hadda
Maimaitawa
Kowane aya
Cikakken madauki
Babban mai karantawa
A ci gaba - Madauki A-B /

Kara Ruku'u 470 na Alkur'ani

Ruku'u 470 daga Surah Al-Waqia ne (ayoyi 39 zuwa 74). Yana ɗauke da ayoyi 36 kuma yana cikin Juz 27.

An sabunta a 10 Yuli 2026 03h52

Ruku 470 dans le Coran

36
ayoyi
1
Surah
27
Juz
v.39 – v.74
Ayoyi

Sourate dans le Ruku 470

Shafi 536
Ruku'u 470
سورة الواقعة
Juz 27 81.2% (324/399)
Hizb 54 63.1% (128/203)

ثُمَّ إِنَّكُمْ أَيُّهَا ٱلضَّآلُّونَ ٱلْمُكَذِّبُونَ ﴿٥١﴾

"Sa'an nan lalle ku, ya kũ ɓatattu, mãsu ƙaryatãwa!"

لَـَٔاكِلُونَ مِن شَجَرٍۢ مِّن زَقُّومٍۢ ﴿٥٢﴾

"Lalle mãsu cĩ ne daga wata itãciya ta zaƙƙum (ɗanyen wutã)."

فَمَالِـُٔونَ مِنْهَا ٱلْبُطُونَ ﴿٥٣﴾

"Har za ku zama mãsu cika cikunna daga gare ta."

فَشَـٰرِبُونَ عَلَيْهِ مِنَ ٱلْحَمِيمِ ﴿٥٤﴾

"Sa'an nan kuma mãsu shã ne, a kan wannan abin cin, daga ruwan zãfi."

فَشَـٰرِبُونَ شُرْبَ ٱلْهِيمِ ﴿٥٥﴾

"Ku zama mãsu shã irin shan rãƙuma mãsu ƙishirwa."

هَـٰذَا نُزُلُهُمْ يَوْمَ ٱلدِّينِ ﴿٥٦﴾

Wannan ita ce liyãfarsu a rãnar sakamako.

نَحْنُ خَلَقْنَـٰكُمْ فَلَوْلَا تُصَدِّقُونَ ﴿٥٧﴾

Mũ ne Muka halitta ku, to, don me bã zã ku gaskata ba?

أَفَرَءَيْتُم مَّا تُمْنُونَ ﴿٥٨﴾

Shin kuma kun ga abin da kuke fitarwa na maniyyi?

ءَأَنتُمْ تَخْلُقُونَهُۥٓ أَمْ نَحْنُ ٱلْخَـٰلِقُونَ ﴿٥٩﴾

Shin kũ ne kuke halitta shi, kõ kuwa mũ ne Mãsu halittãwa?

نَحْنُ قَدَّرْنَا بَيْنَكُمُ ٱلْمَوْتَ وَمَا نَحْنُ بِمَسْبُوقِينَ ﴿٦٠﴾

Mũ ne Muka ƙaddara mutuwa a tsakãninku, kuma ba Mu zama Mãsu gajiyãwa ba,

عَلَىٰٓ أَن نُّبَدِّلَ أَمْثَـٰلَكُمْ وَنُنشِئَكُمْ فِى مَا لَا تَعْلَمُونَ ﴿٦١﴾

A kan Mu musanya waɗansu (mutãne) kamarku, kuma Mu mayar da ku a cikin wata halitta da ba ku sani ba.

وَلَقَدْ عَلِمْتُمُ ٱلنَّشْأَةَ ٱلْأُولَىٰ فَلَوْلَا تَذَكَّرُونَ ﴿٦٢﴾

Kuma lalle, ne haƙĩƙa, kun san halittar farko, to, don me ba zã ku yi tunãni ba?

أَفَرَءَيْتُم مَّا تَحْرُثُونَ ﴿٦٣﴾

Shin, kuma kun ga abin da kũke nõmãwa?

ءَأَنتُمْ تَزْرَعُونَهُۥٓ أَمْ نَحْنُ ٱلزَّٰرِعُونَ ﴿٦٤﴾

Shin, kũ ne ke tsirar da shi kõ kuwa Mũ ne Mãsu tsirarwa?

لَوْ نَشَآءُ لَجَعَلْنَـٰهُ حُطَـٰمًۭا فَظَلْتُمْ تَفَكَّهُونَ ﴿٦٥﴾

Dã Munã so lalle, da Mun sanya shi bũsasshiyar ciyãwa, sai ku yini kunã mãmãkin bãƙin ciki.

إِنَّا لَمُغْرَمُونَ ﴿٦٦﴾

(Kunã cẽwa) "Lalle haƙĩƙa an azã mana tãra!"

بَلْ نَحْنُ مَحْرُومُونَ ﴿٦٧﴾

"Ã'a, mun dai zama waɗanda aka hanã wa!"

أَفَرَءَيْتُمُ ٱلْمَآءَ ٱلَّذِى تَشْرَبُونَ ﴿٦٨﴾

Shin, kuma kun ga ruwa wannan da kuke sha?

ءَأَنتُمْ أَنزَلْتُمُوهُ مِنَ ٱلْمُزْنِ أَمْ نَحْنُ ٱلْمُنزِلُونَ ﴿٦٩﴾

Shin, kũ ne kuke saukar da shi daga girgije, kõ kuwa Mũne Mãsu saukarwa?

لَوْ نَشَآءُ جَعَلْنَـٰهُ أُجَاجًۭا فَلَوْلَا تَشْكُرُونَ ﴿٧٠﴾

Dã Mun so, dã Mun mayar da shi ruwan zartsi. To don me bã ku gõdẽwa?

أَفَرَءَيْتُمُ ٱلنَّارَ ٱلَّتِى تُورُونَ ﴿٧١﴾

Shin, kuma kun ga wutã wannan da kuke ƙyastãwa?

ءَأَنتُمْ أَنشَأْتُمْ شَجَرَتَهَآ أَمْ نَحْنُ ٱلْمُنشِـُٔونَ ﴿٧٢﴾

Shin, kũ ne kuke ƙagã halittar itãciyarta, kõ kuwa Mũ ne Mãsu ƙãgãwa?

نَحْنُ جَعَلْنَـٰهَا تَذْكِرَةًۭ وَمَتَـٰعًۭا لِّلْمُقْوِينَ ﴿٧٣﴾

Mũ ne Muka sanya ta wata abar wa'azi da jin dãɗi ga matafiya a cikin jẽji.

فَسَبِّحْ بِٱسْمِ رَبِّكَ ٱلْعَظِيمِ ﴿٧٤﴾

Sai ka tsarkake sũnan Ubangijinka Mai girma.

بسم الله الرحمن الرحيم Jum 24 Muharram
الجمعة 24 محرّم
هلال متناقص Gajimaren Raguwa Rana 25 / 29.5
Haske 21%
Wata Sabo a cikin kwana 4
سبحان الله Subhanallah - Tsarkin Allah