Kara Ruku'u 470 na Alkur'ani

Ruku'u 470 daga Surah Al-Waqia ne (ayoyi 39 zuwa 74). Yana ɗauke da ayoyi 36 kuma yana cikin Juz 27.

An sabunta a 05 Agusta 2026 16h34

Ruku 470 a cikin Alkur'ani

36
ayoyi
1
Surah
27
Juz
v.39 – v.74
Ayoyi

Surori a cikin Ruku 470

الواقعة · Juz 27
Shafi 535
Ruku'u 470
سورة الواقعة
Juz 27 78.2% (312/399)
Hizb 54 57.1% (116/203)

ثُلَّةٌۭ مِّنَ ٱلْأَوَّلِينَ ﴿٣٩﴾

Wata ƙungiya ce daga mutãnen farko.

وَثُلَّةٌۭ مِّنَ ٱلْـَٔاخِرِينَ ﴿٤٠﴾

Da wata ƙungiya daga mutãnen ƙarshe.

وَأَصْحَـٰبُ ٱلشِّمَالِ مَآ أَصْحَـٰبُ ٱلشِّمَالِ ﴿٤١﴾

Mazõwa hagu, Mẽne ne mazõwa hagu?

فِى سَمُومٍۢ وَحَمِيمٍۢ ﴿٤٢﴾

Sunã a cikin wata iskar zãfi da wani ruwan zãfi.

وَظِلٍّۢ مِّن يَحْمُومٍۢ ﴿٤٣﴾

Da wata inuwa ta hayãƙi mai baƙi.

لَّا بَارِدٍۢ وَلَا كَرِيمٍ ﴿٤٤﴾

Bã mai sanyi ba, kuma bã mai wata ni'ima ba.

إِنَّهُمْ كَانُوا۟ قَبْلَ ذَٰلِكَ مُتْرَفِينَ ﴿٤٥﴾

Lalle sũ, sun kasance a gabãnin wannan waɗanda aka jiyar dãɗi.

وَكَانُوا۟ يُصِرُّونَ عَلَى ٱلْحِنثِ ٱلْعَظِيمِ ﴿٤٦﴾

Kuma sun kasance sunã dõgẽwa a kan mummũnan zunubi mai girma.

وَكَانُوا۟ يَقُولُونَ أَئِذَا مِتْنَا وَكُنَّا تُرَابًۭا وَعِظَـٰمًا أَءِنَّا لَمَبْعُوثُونَ ﴿٤٧﴾

Kuma sun kasance sunã cẽwa: "Shin idan mun mutukuma muko kasance turɓãya da ƙasũsuwa shin lalle mũ waɗanda zã a kõma rãyarwa ne haƙĩƙatan?"

أَوَءَابَآؤُنَا ٱلْأَوَّلُونَ ﴿٤٨﴾

"Shin, kuma da ubanninmu na farko?"

قُلْ إِنَّ ٱلْأَوَّلِينَ وَٱلْـَٔاخِرِينَ ﴿٤٩﴾

Ka ce: "Lalle mutãnen farko da na ƙarshe."

لَمَجْمُوعُونَ إِلَىٰ مِيقَـٰتِ يَوْمٍۢ مَّعْلُومٍۢ ﴿٥٠﴾

"Tabbas, waɗanda ake tãrãwa ne a cikin wani yini sananne."

ثُمَّ إِنَّكُمْ أَيُّهَا ٱلضَّآلُّونَ ٱلْمُكَذِّبُونَ ﴿٥١﴾

"Sa'an nan lalle ku, ya kũ ɓatattu, mãsu ƙaryatãwa!"

لَـَٔاكِلُونَ مِن شَجَرٍۢ مِّن زَقُّومٍۢ ﴿٥٢﴾

"Lalle mãsu cĩ ne daga wata itãciya ta zaƙƙum (ɗanyen wutã)."

فَمَالِـُٔونَ مِنْهَا ٱلْبُطُونَ ﴿٥٣﴾

"Har za ku zama mãsu cika cikunna daga gare ta."

فَشَـٰرِبُونَ عَلَيْهِ مِنَ ٱلْحَمِيمِ ﴿٥٤﴾

"Sa'an nan kuma mãsu shã ne, a kan wannan abin cin, daga ruwan zãfi."

فَشَـٰرِبُونَ شُرْبَ ٱلْهِيمِ ﴿٥٥﴾

"Ku zama mãsu shã irin shan rãƙuma mãsu ƙishirwa."

هَـٰذَا نُزُلُهُمْ يَوْمَ ٱلدِّينِ ﴿٥٦﴾

Wannan ita ce liyãfarsu a rãnar sakamako.

نَحْنُ خَلَقْنَـٰكُمْ فَلَوْلَا تُصَدِّقُونَ ﴿٥٧﴾

Mũ ne Muka halitta ku, to, don me bã zã ku gaskata ba?

أَفَرَءَيْتُم مَّا تُمْنُونَ ﴿٥٨﴾

Shin kuma kun ga abin da kuke fitarwa na maniyyi?

ءَأَنتُمْ تَخْلُقُونَهُۥٓ أَمْ نَحْنُ ٱلْخَـٰلِقُونَ ﴿٥٩﴾

Shin kũ ne kuke halitta shi, kõ kuwa mũ ne Mãsu halittãwa?

نَحْنُ قَدَّرْنَا بَيْنَكُمُ ٱلْمَوْتَ وَمَا نَحْنُ بِمَسْبُوقِينَ ﴿٦٠﴾

Mũ ne Muka ƙaddara mutuwa a tsakãninku, kuma ba Mu zama Mãsu gajiyãwa ba,

عَلَىٰٓ أَن نُّبَدِّلَ أَمْثَـٰلَكُمْ وَنُنشِئَكُمْ فِى مَا لَا تَعْلَمُونَ ﴿٦١﴾

A kan Mu musanya waɗansu (mutãne) kamarku, kuma Mu mayar da ku a cikin wata halitta da ba ku sani ba.

وَلَقَدْ عَلِمْتُمُ ٱلنَّشْأَةَ ٱلْأُولَىٰ فَلَوْلَا تَذَكَّرُونَ ﴿٦٢﴾

Kuma lalle, ne haƙĩƙa, kun san halittar farko, to, don me ba zã ku yi tunãni ba?

أَفَرَءَيْتُم مَّا تَحْرُثُونَ ﴿٦٣﴾

Shin, kuma kun ga abin da kũke nõmãwa?

ءَأَنتُمْ تَزْرَعُونَهُۥٓ أَمْ نَحْنُ ٱلزَّٰرِعُونَ ﴿٦٤﴾

Shin, kũ ne ke tsirar da shi kõ kuwa Mũ ne Mãsu tsirarwa?

لَوْ نَشَآءُ لَجَعَلْنَـٰهُ حُطَـٰمًۭا فَظَلْتُمْ تَفَكَّهُونَ ﴿٦٥﴾

Dã Munã so lalle, da Mun sanya shi bũsasshiyar ciyãwa, sai ku yini kunã mãmãkin bãƙin ciki.

إِنَّا لَمُغْرَمُونَ ﴿٦٦﴾

(Kunã cẽwa) "Lalle haƙĩƙa an azã mana tãra!"

بَلْ نَحْنُ مَحْرُومُونَ ﴿٦٧﴾

"Ã'a, mun dai zama waɗanda aka hanã wa!"

أَفَرَءَيْتُمُ ٱلْمَآءَ ٱلَّذِى تَشْرَبُونَ ﴿٦٨﴾

Shin, kuma kun ga ruwa wannan da kuke sha?

ءَأَنتُمْ أَنزَلْتُمُوهُ مِنَ ٱلْمُزْنِ أَمْ نَحْنُ ٱلْمُنزِلُونَ ﴿٦٩﴾

Shin, kũ ne kuke saukar da shi daga girgije, kõ kuwa Mũne Mãsu saukarwa?

لَوْ نَشَآءُ جَعَلْنَـٰهُ أُجَاجًۭا فَلَوْلَا تَشْكُرُونَ ﴿٧٠﴾

Dã Mun so, dã Mun mayar da shi ruwan zartsi. To don me bã ku gõdẽwa?

أَفَرَءَيْتُمُ ٱلنَّارَ ٱلَّتِى تُورُونَ ﴿٧١﴾

Shin, kuma kun ga wutã wannan da kuke ƙyastãwa?

ءَأَنتُمْ أَنشَأْتُمْ شَجَرَتَهَآ أَمْ نَحْنُ ٱلْمُنشِـُٔونَ ﴿٧٢﴾

Shin, kũ ne kuke ƙagã halittar itãciyarta, kõ kuwa Mũ ne Mãsu ƙãgãwa?

نَحْنُ جَعَلْنَـٰهَا تَذْكِرَةًۭ وَمَتَـٰعًۭا لِّلْمُقْوِينَ ﴿٧٣﴾

Mũ ne Muka sanya ta wata abar wa'azi da jin dãɗi ga matafiya a cikin jẽji.

فَسَبِّحْ بِٱسْمِ رَبِّكَ ٱلْعَظِيمِ ﴿٧٤﴾

Sai ka tsarkake sũnan Ubangijinka Mai girma.

بسم الله الرحمن الرحيم Tal 11 Rabi' al-Awwal
الثلاثاء 11 ربيع الأول
أحدب متزايد Cikakken Wata Tasowa Rana 11.7 / 29.5
Haske 89%
Cikakken Wata a cikin kwana 3
أستغفر الله Ina neman gafara daga Allah