الواقعة · Juz 27
Tafi zuwa
Alamomi
Mai karantawa / Qārī
Gudun sauti
Maimaita aya
Maimaita
Gungumewa kai
Fassara

Abubakar Mahmoud Gumi

Fontin larabci
Girman rubutu
Larabci
Fassara
Zangin da za a hadda
Maimaitawa
Kowane aya
Cikakken madauki
Babban mai karantawa
A ci gaba - Madauki A-B /

Kara Ruku'u 471 na Alkur'ani

Ruku'u 471 daga Surah Al-Waqia ne (ayoyi 75 zuwa 96). Yana ɗauke da ayoyi 22 kuma yana cikin Juz 27.

An sabunta a 10 Yuli 2026 03h52

Ruku 471 dans le Coran

22
ayoyi
1
Surah
27
Juz
v.75 – v.96
Ayoyi

Sourate dans le Ruku 471

Shafi 537
Ruku'u 471
سورة الواقعة
Juz 27 87.7% (350/399)
Hizb 54 75.9% (154/203)

إِنَّهُۥ لَقُرْءَانٌۭ كَرِيمٌۭ ﴿٧٧﴾

Lalle shi (wannan littãfi), haƙĩƙa, abin karantãwa ne mai daraja.

فِى كِتَـٰبٍۢ مَّكْنُونٍۢ ﴿٧٨﴾

A cikin wani littafi tsararre.

لَّا يَمَسُّهُۥٓ إِلَّا ٱلْمُطَهَّرُونَ ﴿٧٩﴾

Bãbu mai shãfa shi fãce waɗanda aka tsarkake.

تَنزِيلٌۭ مِّن رَّبِّ ٱلْعَـٰلَمِينَ ﴿٨٠﴾

Wanda aka saukar ne daga Ubangijin halitta.

أَفَبِهَـٰذَا ٱلْحَدِيثِ أَنتُم مُّدْهِنُونَ ﴿٨١﴾

Shin, to, wannan lãbãrin ne kuke mãsu wulãkantãwa?

وَتَجْعَلُونَ رِزْقَكُمْ أَنَّكُمْ تُكَذِّبُونَ ﴿٨٢﴾

Kuma kunã sanya arzikinku (game da shi) lalle kũ, ku ƙaryata (shi)?

فَلَوْلَآ إِذَا بَلَغَتِ ٱلْحُلْقُومَ ﴿٨٣﴾

To, don me idan rai ya kai ga maƙõshi? (Kusa da mutuwa).

وَأَنتُمْ حِينَئِذٍۢ تَنظُرُونَ ﴿٨٤﴾

Alhãli kuwa kũ, a lõklcin nan, kunã kallo.

وَنَحْنُ أَقْرَبُ إِلَيْهِ مِنكُمْ وَلَـٰكِن لَّا تُبْصِرُونَ ﴿٨٥﴾

Kuma Mũ ne mafi kusanta gare shi daga gare ku, to, amma kũ bã ku gani.

فَلَوْلَآ إِن كُنتُمْ غَيْرَ مَدِينِينَ ﴿٨٦﴾

To, don me in dai kun kasance bã waɗanda zã a yi wa sakamako ba?

تَرْجِعُونَهَآ إِن كُنتُمْ صَـٰدِقِينَ ﴿٨٧﴾

Ku mayar da shi (cikin jikinsa) har idan kun kasance mãsu gaskiya.

فَأَمَّآ إِن كَانَ مِنَ ٱلْمُقَرَّبِينَ ﴿٨٨﴾

To, amma idan (mai mutuwar) ya kasance daga makusanta,

فَرَوْحٌۭ وَرَيْحَانٌۭ وَجَنَّتُ نَعِيمٍۢ ﴿٨٩﴾

Sai hũtawa da kyakkyawan abinci da Aljannar ni'ima.

وَأَمَّآ إِن كَانَ مِنْ أَصْحَـٰبِ ٱلْيَمِينِ ﴿٩٠﴾

Kuma amma idan ya kasance daga mazõwa dãma,

فَسَلَـٰمٌۭ لَّكَ مِنْ أَصْحَـٰبِ ٱلْيَمِينِ ﴿٩١﴾

Sai (a ce masa) aminci ya tabbata a gare ka daga mazõwa dãma.

وَأَمَّآ إِن كَانَ مِنَ ٱلْمُكَذِّبِينَ ٱلضَّآلِّينَ ﴿٩٢﴾

Kuma amma idan ya kasance daga mãsu ƙaryatãwar, ɓatattun,

فَنُزُلٌۭ مِّنْ حَمِيمٍۢ ﴿٩٣﴾

Sai wata liyãfa ta ruwan zãfi.

وَتَصْلِيَةُ جَحِيمٍ ﴿٩٤﴾

Da ƙõnuwa da Jahĩm,

إِنَّ هَـٰذَا لَهُوَ حَقُّ ٱلْيَقِينِ ﴿٩٥﴾

Lalle wannan, haƙĩƙa, ita ce gaskiya ta yaƙĩni.

فَسَبِّحْ بِٱسْمِ رَبِّكَ ٱلْعَظِيمِ ﴿٩٦﴾

Sabõda haka, ka tsarkake sũnan Ubangijinka, Mai karimci.

بسم الله الرحمن الرحيم Jum 24 Muharram
الجمعة 24 محرّم
هلال متناقص Gajimaren Raguwa Rana 25 / 29.5
Haske 21%
Wata Sabo a cikin kwana 4
الحمد لله Alhamdulillah - Godiya ta tabbata ga Allah