الحاقة · Juz 29
Tafi zuwa
Alamomi
Mai karantawa / Qārī
Gudun sauti
Maimaita aya
Maimaita
Gungumewa kai
Fassara

Abubakar Mahmoud Gumi

Fontin larabci
Girman rubutu
Larabci
Fassara
Zangin da za a hadda
Maimaitawa
Kowane aya
Cikakken madauki
Babban mai karantawa
A ci gaba - Madauki A-B /

Kara Ruku'u 501 na Alkur'ani

Ruku'u 501 daga Surah Al-Haqqa ne (ayoyi 38 zuwa 52). Yana ɗauke da ayoyi 15 kuma yana cikin Juz 29.

An sabunta a 10 Yuli 2026 03h52

Ruku 501 dans le Coran

15
ayoyi
1
Surah
29
Juz
v.38 – v.52
Ayoyi

Sourate dans le Ruku 501

Shafi 568
Ruku'u 501
سورة الحاقة
Juz 29 27.6% (119/431)
Hizb 57 57.8% (119/206)

فَلَآ أُقْسِمُ بِمَا تُبْصِرُونَ ﴿٣٨﴾

To, ba sai Nã yi rantsuwa da abin da kuke iya gani ba,

وَمَا لَا تُبْصِرُونَ ﴿٣٩﴾

Da abin da bã ku iya gani.

إِنَّهُۥ لَقَوْلُ رَسُولٍۢ كَرِيمٍۢ ﴿٤٠﴾

Lalle ne, shi (Alƙur'ani) tabbas maganar wani manzo (Jibirilu) mai daraja ne.

وَمَا هُوَ بِقَوْلِ شَاعِرٍۢ ۚ قَلِيلًۭا مَّا تُؤْمِنُونَ ﴿٤١﴾

Kuma shi ba maganar wani mawãƙi ba ne. Kaɗan ƙwarai zã ku gaskata.

وَلَا بِقَوْلِ كَاهِنٍۢ ۚ قَلِيلًۭا مَّا تَذَكَّرُونَ ﴿٤٢﴾

Kuma bã maganar bõka ba ne. Kaɗan ƙwarai zã ku iya tunãwa.

تَنزِيلٌۭ مِّن رَّبِّ ٱلْعَـٰلَمِينَ ﴿٤٣﴾

Abin saukarwã ne daga Ubangijin halitta duka.

وَلَوْ تَقَوَّلَ عَلَيْنَا بَعْضَ ٱلْأَقَاوِيلِ ﴿٤٤﴾

Kuma dã (Muhammadu) yã faɗi wata maganã, yã jingina ta garẽ Mu.

لَأَخَذْنَا مِنْهُ بِٱلْيَمِينِ ﴿٤٥﴾

Dã Mun kãma shi da dãma.

ثُمَّ لَقَطَعْنَا مِنْهُ ٱلْوَتِينَ ﴿٤٦﴾

sa'an nan, lalle ne, dã Mun kãtse masa lakã.

فَمَا مِنكُم مِّنْ أَحَدٍ عَنْهُ حَـٰجِزِينَ ﴿٤٧﴾

Kuma daga cikinku bãbu wasu mãsu iya kãre (azãbarMu) daga gare shi.

وَإِنَّهُۥ لَتَذْكِرَةٌۭ لِّلْمُتَّقِينَ ﴿٤٨﴾

Kuma lalle ne shi (Alƙur'ãni) tanãtarwa ce ga mãsu taƙawa.

وَإِنَّا لَنَعْلَمُ أَنَّ مِنكُم مُّكَذِّبِينَ ﴿٤٩﴾

Kuma lalle, ne Mũ, wallahi Munã sane da cẽwa daga cikinku alwwai mãsu ƙaryatãwa.

وَإِنَّهُۥ لَحَسْرَةٌ عَلَى ٱلْكَـٰفِرِينَ ﴿٥٠﴾

Kuma lalle ne shi (Alƙarãni) wallahi baƙin ciki ne ga kãfirai.

وَإِنَّهُۥ لَحَقُّ ٱلْيَقِينِ ﴿٥١﴾

Kuma lalle, ne shi gaskiya ce ta yaƙshẽni.

فَسَبِّحْ بِٱسْمِ رَبِّكَ ٱلْعَظِيمِ ﴿٥٢﴾

Sabõda haka, ka tsarkake sũnan Ubangjinka, mai girma.

بسم الله الرحمن الرحيم Jum 24 Muharram
الجمعة 24 محرّم
هلال متناقص Gajimaren Raguwa Rana 25 / 29.5
Haske 21%
Wata Sabo a cikin kwana 4
الحمد لله Alhamdulillah - Godiya ta tabbata ga Allah