المعارج · Juz 29
Tafi zuwa
Alamomi
Mai karantawa / Qārī
Gudun sauti
Maimaita aya
Maimaita
Gungumewa kai
Fassara

Abubakar Mahmoud Gumi

Fontin larabci
Girman rubutu
Larabci
Fassara
Zangin da za a hadda
Maimaitawa
Kowane aya
Cikakken madauki
Babban mai karantawa
A ci gaba - Madauki A-B /

Kara Ruku'u 502 na Alkur'ani

Ruku'u 502 daga Surah Al-Maarij ne (ayoyi 1 zuwa 35). Yana ɗauke da ayoyi 35 kuma yana cikin Juz 29.

An sabunta a 10 Yuli 2026 03h52

Ruku 502 dans le Coran

35
ayoyi
1
Surah
29
Juz
v.1 – v.35
Ayoyi

Sourate dans le Ruku 502

Shafi 569
Ruku'u 502
سورة المعارج
Juz 29 33.4% (144/431)
Hizb 57 69.9% (144/206)

يُبَصَّرُونَهُمْ ۚ يَوَدُّ ٱلْمُجْرِمُ لَوْ يَفْتَدِى مِنْ عَذَابِ يَوْمِئِذٍۭ بِبَنِيهِ ﴿١١﴾

Ana sanya su, su gajũna, mai laifi na gũrin dã zai iya yin fansa, daga azãbar rãnar nan, da ɗiyansa,

وَصَـٰحِبَتِهِۦ وَأَخِيهِ ﴿١٢﴾

Da matarsa da ɗan'uwansa.

وَفَصِيلَتِهِ ٱلَّتِى تُـْٔوِيهِ ﴿١٣﴾

Da danginsa, mãsu tattarã shi.

وَمَن فِى ٱلْأَرْضِ جَمِيعًۭا ثُمَّ يُنجِيهِ ﴿١٤﴾

Da wanda ke a cikin dũniya duka gabã ɗaya, sa'an nan fansar, ta tsĩrar da shi.

كَلَّآ ۖ إِنَّهَا لَظَىٰ ﴿١٥﴾

A'aha! Lalle ne fa, ita ce Lazã,

نَزَّاعَةًۭ لِّلشَّوَىٰ ﴿١٦﴾

Mai twãle fãtar goshi.

تَدْعُوا۟ مَنْ أَدْبَرَ وَتَوَلَّىٰ ﴿١٧﴾

Tanã kiran wanda ya jũya bãya (daga addini) kuma ya kau da kai.

وَجَمَعَ فَأَوْعَىٰٓ ﴿١٨﴾

Ya tãra (dũkiya), kuma ya sanya ta a cikin jaka.

۞ إِنَّ ٱلْإِنسَـٰنَ خُلِقَ هَلُوعًا ﴿١٩﴾

Lalle ne mutum an halitta shi mai ciwon kwaɗayi.

إِذَا مَسَّهُ ٱلشَّرُّ جَزُوعًۭا ﴿٢٠﴾

Idan sharri ya shãfe shi, ya kãsa haƙuri.

وَإِذَا مَسَّهُ ٱلْخَيْرُ مَنُوعًا ﴿٢١﴾

Kuma idan alhẽri ya shãfe shi, ya yi rõwa.

إِلَّا ٱلْمُصَلِّينَ ﴿٢٢﴾

Sai mãsu yin salla,

ٱلَّذِينَ هُمْ عَلَىٰ صَلَاتِهِمْ دَآئِمُونَ ﴿٢٣﴾

Waɗanda suke, a kan sallarsu, su, mãsu dawwama ne.

وَٱلَّذِينَ فِىٓ أَمْوَٰلِهِمْ حَقٌّۭ مَّعْلُومٌۭ ﴿٢٤﴾

Kuma waɗanda a cikin dũkiyarsu, akwai wani haƙƙi sananne.

لِّلسَّآئِلِ وَٱلْمَحْرُومِ ﴿٢٥﴾

Ga (matalauci) mai rõƙo da wanda aka hanã wa roƙon.

وَٱلَّذِينَ يُصَدِّقُونَ بِيَوْمِ ٱلدِّينِ ﴿٢٦﴾

Da waɗannan da ke gaskata rãnar sakamako.

وَٱلَّذِينَ هُم مِّنْ عَذَابِ رَبِّهِم مُّشْفِقُونَ ﴿٢٧﴾

Da waɗannan sabõda azãbar Ubangijinsu, suna jin tsõro.

إِنَّ عَذَابَ رَبِّهِمْ غَيْرُ مَأْمُونٍۢ ﴿٢٨﴾

Lalle ne, azãbar Ubangijinsu bã wadda ake iya amincẽwaba ce.

وَٱلَّذِينَ هُمْ لِفُرُوجِهِمْ حَـٰفِظُونَ ﴿٢٩﴾

Da waɗanda suke, ga farjojinsu, mãsu tsarewa ne.

إِلَّا عَلَىٰٓ أَزْوَٰجِهِمْ أَوْ مَا مَلَكَتْ أَيْمَـٰنُهُمْ فَإِنَّهُمْ غَيْرُ مَلُومِينَ ﴿٣٠﴾

Sai fa a kan matan aurensu da abin da hannayensu na dãma suka mallaka. To lalle ne sũkam ba waɗanda ake zargi ba ne.

فَمَنِ ٱبْتَغَىٰ وَرَآءَ ذَٰلِكَ فَأُو۟لَـٰٓئِكَ هُمُ ٱلْعَادُونَ ﴿٣١﴾

To, duk wanda ya nẽmi abin da yake a bayan wannan, to, waɗancan sũ ne mãsu ƙetare iyãka.

وَٱلَّذِينَ هُمْ لِأَمَـٰنَـٰتِهِمْ وَعَهْدِهِمْ رَٰعُونَ ﴿٣٢﴾

Kuma da waɗannan da suke ga amãnõninsu da alkawarinsu mãsu tsarẽwa ne.

وَٱلَّذِينَ هُم بِشَهَـٰدَٰتِهِمْ قَآئِمُونَ ﴿٣٣﴾

Kuma da waɗanda suke, ga shaidarsu, mãsu dãgẽwa ne.

وَٱلَّذِينَ هُمْ عَلَىٰ صَلَاتِهِمْ يُحَافِظُونَ ﴿٣٤﴾

Kuma waɗanda suke, a kan sallarsu, mãsu tsarẽwa ne.

أُو۟لَـٰٓئِكَ فِى جَنَّـٰتٍۢ مُّكْرَمُونَ ﴿٣٥﴾

Waɗannan, a cikin gidãjen Aljanna, waɗanda ake girmamãwa ne

بسم الله الرحمن الرحيم Jum 24 Muharram
الجمعة 24 محرّم
هلال متناقص Gajimaren Raguwa Rana 25 / 29.5
Haske 21%
Wata Sabo a cikin kwana 4
الحمد لله Alhamdulillah - Godiya ta tabbata ga Allah