Kara Shafi 372 na Alkur'ani

Shafi 372 na Mushaf yana ɗauke da ayoyi 25. Yana cikin Juz 19, Hizb 38.

An sabunta a 05 Agusta 2026 16h34

Shafi 372 a cikin Alkur'ani

25
ayoyi
19
Juz
38
Hizb
1
Surah

Surori a cikin Shafi 372

الشعراء · Juz 19
Kewaya
Alamomi
Sauti
Hadda
Nuni
Juz 19
Shafi 372
سورة الشعراء
Juz 19 49.6% (168/339)
Hizb 38 0.6% (1/172)

قَالَ وَمَا عِلْمِى بِمَا كَانُوا۟ يَعْمَلُونَ ﴿112﴾

Ya ce: "Kuma bã ni da sani ga abin da suka kasance sanã aikatãwa."

إِنْ حِسَابُهُمْ إِلَّا عَلَىٰ رَبِّى ۖ لَوْ تَشْعُرُونَ ﴿113﴾

"Hisãbinsu bai zama ba fãce ga Ubangijina, dã kunã sansancẽwa."

وَمَآ أَنَا۠ بِطَارِدِ ٱلْمُؤْمِنِينَ ﴿114﴾

"Ban zama mai kõre mũminai ba."

إِنْ أَنَا۠ إِلَّا نَذِيرٌۭ مُّبِينٌۭ ﴿115﴾

"Nĩ ba kõwa ba ne sai mai gargaɗi mai bayyanãwa."

قَالُوا۟ لَئِن لَّمْ تَنتَهِ يَـٰنُوحُ لَتَكُونَنَّ مِنَ ٱلْمَرْجُومِينَ ﴿116﴾

Suka ce: "Lalle ne, idan ba ka hanu ba, yã Nũhu, (daga maganarka,) haƙĩƙa, kanã kasancẽwa daga waɗanda ake jẽfewa"

قَالَ رَبِّ إِنَّ قَوْمِى كَذَّبُونِ ﴿117﴾

Ya ce: "Yã Ubangijĩna! Lalle ne mutãnena sun ƙaryatã ni."

فَٱفْتَحْ بَيْنِى وَبَيْنَهُمْ فَتْحًۭا وَنَجِّنِى وَمَن مَّعِىَ مِنَ ٱلْمُؤْمِنِينَ ﴿118﴾

"Sai ka yi hukunci, a tsakãnĩna da tsakãninsu tabbataccen hukanci, kuma ka tsĩrar da ni, da waɗanda suke tãre da ni daga mũminai."

فَأَنجَيْنَـٰهُ وَمَن مَّعَهُۥ فِى ٱلْفُلْكِ ٱلْمَشْحُونِ ﴿119﴾

Sai Muka tsĩrar da shi, shi da waɗanda suke tãre da shi, a cikin jirgi wanda aka yi wa lõdi.

ثُمَّ أَغْرَقْنَا بَعْدُ ٱلْبَاقِينَ ﴿120﴾

Sa'an nan Muka nutsar a bãyan haka, da sauran.

إِنَّ فِى ذَٰلِكَ لَـَٔايَةًۭ ۖ وَمَا كَانَ أَكْثَرُهُم مُّؤْمِنِينَ ﴿121﴾

Lalle ne a cikin wannan akwai ãyã, kuma mafi yawansu, ba su kasance mãsu ĩmãni ba.

وَإِنَّ رَبَّكَ لَهُوَ ٱلْعَزِيزُ ٱلرَّحِيمُ ﴿122﴾

Kuma Lalle ne, Ubangijinka, haƙĩƙa, Shĩ ne Mabuwãyi, Mai Rahama.

كَذَّبَتْ عَادٌ ٱلْمُرْسَلِينَ ﴿123﴾

Ãdãwa sun ƙaryata Manzanni.

إِذْ قَالَ لَهُمْ أَخُوهُمْ هُودٌ أَلَا تَتَّقُونَ ﴿124﴾

A lõkacin da ɗan'uwansu, Hũdu ya ce musu, "Bã zã ku yi taƙawa ba?"

إِنِّى لَكُمْ رَسُولٌ أَمِينٌۭ ﴿125﴾

"Lalle ne ni, zuwa gare ku, haƙĩƙa, Manzo ne, amintacce."

فَٱتَّقُوا۟ ٱللَّهَ وَأَطِيعُونِ ﴿126﴾

"Sabõda haka ku bi Allah da taƙawa, kuma ku yi mini ɗã'ã."

وَمَآ أَسْـَٔلُكُمْ عَلَيْهِ مِنْ أَجْرٍ ۖ إِنْ أَجْرِىَ إِلَّا عَلَىٰ رَبِّ ٱلْعَـٰلَمِينَ ﴿127﴾

"Kuma bã ni tambayar wata ijãra a kansa. Ijãrãta ba ta zama ba, fãce daga Ubangijin halittu."

أَتَبْنُونَ بِكُلِّ رِيعٍ ءَايَةًۭ تَعْبَثُونَ ﴿128﴾

"Shin, kunã yin ginin sitadiyo a kõwane tsauni ne, kunã yin wãsa?"

وَتَتَّخِذُونَ مَصَانِعَ لَعَلَّكُمْ تَخْلُدُونَ ﴿129﴾

"Kuma kunã riƙon matsãrar ruwa, tsammãninku, ku dawwama?"

وَإِذَا بَطَشْتُم بَطَشْتُمْ جَبَّارِينَ ﴿130﴾

"Kuma idan kun yi damƙa, sai ku yi damƙar kunã mãsu tanƙwasãwa."

فَٱتَّقُوا۟ ٱللَّهَ وَأَطِيعُونِ ﴿131﴾

"To ku bi Allah da taƙawa, kuma ku yi mini ɗã'ã."

وَٱتَّقُوا۟ ٱلَّذِىٓ أَمَدَّكُم بِمَا تَعْلَمُونَ ﴿132﴾

"Ku ji tsõron wanda Ya taimake ku da abin da kuka sani."

أَمَدَّكُم بِأَنْعَـٰمٍۢ وَبَنِينَ ﴿133﴾

"Ya taimake ku da dabbõbin ni'ima da ɗiya."

وَجَنَّـٰتٍۢ وَعُيُونٍ ﴿134﴾

"Da gõnaki da marẽmari."

إِنِّىٓ أَخَافُ عَلَيْكُمْ عَذَابَ يَوْمٍ عَظِيمٍۢ ﴿135﴾

"Lalle ne nĩ, inã ji muku tsõron azãbar wani yini mai girma."

قَالُوا۟ سَوَآءٌ عَلَيْنَآ أَوَعَظْتَ أَمْ لَمْ تَكُن مِّنَ ٱلْوَٰعِظِينَ ﴿136﴾

Suka ce: "Daidai ne a kanmu: Kã yi wa'azi kõ ba ka kasance daga mãsu wa'azi ba."

بسم الله الرحمن الرحيم Lah 7 Rabi' al-Thani
الأحد 7 ربيع الآخر
التربيع الأول Kwata na Farko Rana 8.3 / 29.5
Haske 59%
Cikakken Wata a cikin kwana 6
لا حول ولا قوة إلا بالله Babu wata ƙarfi ko iko sai na Allah