Kara Shafi 375 na Alkur'ani

Shafi 375 na Mushaf yana ɗauke da ayoyi 23. Yana cikin Juz 19, Hizb 38.

An sabunta a 05 Agusta 2026 16h34

Shafi 375 a cikin Alkur'ani

23
ayoyi
19
Juz
38
Hizb
1
Surah

Surori a cikin Shafi 375

الشعراء · Juz 19
Kewaya
Alamomi
Sauti
Hadda
Nuni
Juz 19
Shafi 375
سورة الشعراء
Juz 19 70.8% (240/339)
Hizb 38 42.4% (73/172)

وَٱتَّقُوا۟ ٱلَّذِى خَلَقَكُمْ وَٱلْجِبِلَّةَ ٱلْأَوَّلِينَ ﴿184﴾

"Kuma ku ji tsõron Allah wanda Ya halitta ku, kũ da jama'ar farko."

قَالُوٓا۟ إِنَّمَآ أَنتَ مِنَ ٱلْمُسَحَّرِينَ ﴿185﴾

Suka ce: "Kai dai daga waɗanda suke sihirtattu kawai ne."

وَمَآ أَنتَ إِلَّا بَشَرٌۭ مِّثْلُنَا وَإِن نَّظُنُّكَ لَمِنَ ٱلْكَـٰذِبِينَ ﴿186﴾

"Kuma bã kõwa kake ba, fãce mutum kamarmu kuma lalle ne munã zaton ka, haƙĩƙa, daga maƙaryata."

فَأَسْقِطْ عَلَيْنَا كِسَفًۭا مِّنَ ٱلسَّمَآءِ إِن كُنتَ مِنَ ٱلصَّـٰدِقِينَ ﴿187﴾

"To ka jẽfo wani ɓaɓɓake daga sama a kanmu, idan ka kasance daga mãsu gaskiya."

قَالَ رَبِّىٓ أَعْلَمُ بِمَا تَعْمَلُونَ ﴿188﴾

Ya ce: "Ubangijĩna ne Mafi sani ga abin da kuke aikatãwa."

فَكَذَّبُوهُ فَأَخَذَهُمْ عَذَابُ يَوْمِ ٱلظُّلَّةِ ۚ إِنَّهُۥ كَانَ عَذَابَ يَوْمٍ عَظِيمٍ ﴿189﴾

Sai suka ƙaiyatã shi, sabõda haka, azãbar rãnar girgije ta kãma su. Lalle ne ita, tã kasance azãbar yini mai girma.

إِنَّ فِى ذَٰلِكَ لَـَٔايَةًۭ ۖ وَمَا كَانَ أَكْثَرُهُم مُّؤْمِنِينَ ﴿190﴾

Lalle a cikin wancan haƙĩka akwai ãya, amma mafi yawansu ba su kasance mãsu ĩmãni ba.

وَإِنَّ رَبَّكَ لَهُوَ ٱلْعَزِيزُ ٱلرَّحِيمُ ﴿191﴾

Kuma lalle Ubangijĩnka, haƙĩƙa, Shĩ ne Mabuwãyi, Mai jin ƙai.

وَإِنَّهُۥ لَتَنزِيلُ رَبِّ ٱلْعَـٰلَمِينَ ﴿192﴾

Kuma lalle shi (Alƙur'ãni), haƙĩƙa, saukarwar Ubangijinhalittu ne.

نَزَلَ بِهِ ٱلرُّوحُ ٱلْأَمِينُ ﴿193﴾

Rũhi amintacce ne ya sauka da shi.

عَلَىٰ قَلْبِكَ لِتَكُونَ مِنَ ٱلْمُنذِرِينَ ﴿194﴾

A kan zũciyarka, dõmin ka kasance daga mãsu gargaɗi.

بِلِسَانٍ عَرَبِىٍّۢ مُّبِينٍۢ ﴿195﴾

Da harshe na Larabci mai bayãni.

وَإِنَّهُۥ لَفِى زُبُرِ ٱلْأَوَّلِينَ ﴿196﴾

Kuma lalle shin, haƙĩƙa, yanã a cikin litattafan (Manzannin) farko.

أَوَلَمْ يَكُن لَّهُمْ ءَايَةً أَن يَعْلَمَهُۥ عُلَمَـٰٓؤُا۟ بَنِىٓ إِسْرَٰٓءِيلَ ﴿197﴾

Ashe, bai kasance ãyã ba a gare su, ya zama Mãlaman Banĩ Isrã'ĩla sun san shi?

وَلَوْ نَزَّلْنَـٰهُ عَلَىٰ بَعْضِ ٱلْأَعْجَمِينَ ﴿198﴾

Kuma dã mun saukar da shi a kan sãshen Ajamãwa,

فَقَرَأَهُۥ عَلَيْهِم مَّا كَانُوا۟ بِهِۦ مُؤْمِنِينَ ﴿199﴾

Ya karanta shi a kansu, ba su kasance sabõda shi mãsu ĩmãni ba.

كَذَٰلِكَ سَلَكْنَـٰهُ فِى قُلُوبِ ٱلْمُجْرِمِينَ ﴿200﴾

Kamar wancan ne! Muka shigar da shi a cikin zukãtan mãsu laifi.

لَا يُؤْمِنُونَ بِهِۦ حَتَّىٰ يَرَوُا۟ ٱلْعَذَابَ ٱلْأَلِيمَ ﴿201﴾

Bã zã su yi ĩmãni da shĩ ba sai sun ga azãbar nan mai raɗadi.

فَيَأْتِيَهُم بَغْتَةًۭ وَهُمْ لَا يَشْعُرُونَ ﴿202﴾

Sai ta taho musu kwatsam, alhãli kuwa sũ, ba su sansance ba.

فَيَقُولُوا۟ هَلْ نَحْنُ مُنظَرُونَ ﴿203﴾

Sai su ce: "Shin, mu waɗanda ake yi wa jinkiri ne?"

أَفَبِعَذَابِنَا يَسْتَعْجِلُونَ ﴿204﴾

Ashe, to, da azãbarMu suke nẽman gaggãwa?

أَفَرَءَيْتَ إِن مَّتَّعْنَـٰهُمْ سِنِينَ ﴿205﴾

Ashe, to, kã gani, idan Muka jĩshe su daɗi a shẽkaru,

ثُمَّ جَآءَهُم مَّا كَانُوا۟ يُوعَدُونَ ﴿206﴾

Sa'an nan abin da suka kasance anã yi musu wa'adi (da shi) ya jẽ musu,

بسم الله الرحمن الرحيم Lah 7 Rabi' al-Thani
الأحد 7 ربيع الآخر
التربيع الأول Kwata na Farko Rana 8.3 / 29.5
Haske 60%
Cikakken Wata a cikin kwana 6
الحمد لله Alhamdulillah - Godiya ta tabbata ga Allah