Kara Shafi 528 na Alkur'ani

Shafi 528 na Mushaf yana ɗauke da ayoyi 24. Yana cikin Juz 27, Hizb 53.

An sabunta a 05 Agusta 2026 16h34

Shafi 528 a cikin Alkur'ani

24
ayoyi
27
Juz
53
Hizb
2
Surah
النجم · Juz 27
Juz 27
Shafi 528
سورة النجم
Juz 27 30.8% (123/399)
Hizb 53 62.8% (123/196)

وَأَنَّهُۥ خَلَقَ ٱلزَّوْجَيْنِ ٱلذَّكَرَ وَٱلْأُنثَىٰ ﴿٤٥﴾

Kuma lalle Shĩ ne Ya yi halitta nau'i-nau'i, namiji da mace.

مِن نُّطْفَةٍ إِذَا تُمْنَىٰ ﴿٤٦﴾

Daga wani ɗigon ruwa guda a lõkacin da ake jẽfa shi a cikin mahaifa.

وَأَنَّ عَلَيْهِ ٱلنَّشْأَةَ ٱلْأُخْرَىٰ ﴿٤٧﴾

Kuma a kansa ne ƙãga halitta ta biyu take.

وَأَنَّهُۥ هُوَ أَغْنَىٰ وَأَقْنَىٰ ﴿٤٨﴾

Kuma lalle, Shĩ, Shĩ ne Ya azurta, kuma Ya wadãtar.

وَأَنَّهُۥ هُوَ رَبُّ ٱلشِّعْرَىٰ ﴿٤٩﴾

Kuma lalle, Shĩ, Shi ne Ubangijin Shi'ira.

وَأَنَّهُۥٓ أَهْلَكَ عَادًا ٱلْأُولَىٰ ﴿٥٠﴾

Kuma lalle, Shĩ, Shĩ ne Ya halaka Ãdãwa na farko.

وَثَمُودَا۟ فَمَآ أَبْقَىٰ ﴿٥١﴾

Da Samũdãwa, sa'an nan bai rage su ba.

وَقَوْمَ نُوحٍۢ مِّن قَبْلُ ۖ إِنَّهُمْ كَانُوا۟ هُمْ أَظْلَمَ وَأَطْغَىٰ ﴿٥٢﴾

Da mutãnen Nũhu a gabãnin haka, lalle sũ sun kasance mafi zãlunci kuma mafi girman kai.

وَٱلْمُؤْتَفِكَةَ أَهْوَىٰ ﴿٥٣﴾

Da waɗanda aka birkice ƙasarsu, Ya kãyar da su.

فَغَشَّىٰهَا مَا غَشَّىٰ ﴿٥٤﴾

Sa'an nan abin da ya rufe su, ya rufe su.

فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكَ تَتَمَارَىٰ ﴿٥٥﴾

To, da wace daga ni'imõmin Ubangijinka kake yin shakka?

هَـٰذَا نَذِيرٌۭ مِّنَ ٱلنُّذُرِ ٱلْأُولَىٰٓ ﴿٥٦﴾

wannan (Muhammadu) mai gargaɗi ne kamar irin mãsu gargaɗi na farko.

أَزِفَتِ ٱلْـَٔازِفَةُ ﴿٥٧﴾

Makusanciya fa, tã yi kusa.

لَيْسَ لَهَا مِن دُونِ ٱللَّهِ كَاشِفَةٌ ﴿٥٨﴾

Bãbu wani rai, banda Allah, mai iya bãyani gare ta.

أَفَمِنْ هَـٰذَا ٱلْحَدِيثِ تَعْجَبُونَ ﴿٥٩﴾

Shin, kuma daga wannan lãbãri kuke mãmãki?

وَتَضْحَكُونَ وَلَا تَبْكُونَ ﴿٦٠﴾

Kuma kunã yin dãriya, kuma bã ku yin kũka?

وَأَنتُمْ سَـٰمِدُونَ ﴿٦١﴾

Alhãli kunã mãsu wãsã?

فَٱسْجُدُوا۟ لِلَّهِ وَٱعْبُدُوا۟ ۩ ﴿٦٢﴾

To, ku yi tawãli'u ga Allah, kuma ku bauta (masa).

ٱقْتَرَبَتِ ٱلسَّاعَةُ وَٱنشَقَّ ٱلْقَمَرُ ﴿١﴾

Sã'a ta yi kusa, kuma wata ya tsãge.

وَإِن يَرَوْا۟ ءَايَةًۭ يُعْرِضُوا۟ وَيَقُولُوا۟ سِحْرٌۭ مُّسْتَمِرٌّۭ ﴿٢﴾

Kuma idan sun ga wata ãyã, sai su juya baya su ce: "Sihiri ne mai dõgẽwa!"

وَكَذَّبُوا۟ وَٱتَّبَعُوٓا۟ أَهْوَآءَهُمْ ۚ وَكُلُّ أَمْرٍۢ مُّسْتَقِرٌّۭ ﴿٣﴾

Kuma suka ƙaryata, kuma suka bi son zũciyarsu, alhãli kuwa kõwane al'amari (wanda suke son su tũre daga Annabi) an tabbatar da shi.

وَلَقَدْ جَآءَهُم مِّنَ ٱلْأَنۢبَآءِ مَا فِيهِ مُزْدَجَرٌ ﴿٤﴾

Kuma lalle, abin da yake akwai tsãwatarwa a cikinsa na lãbãraiya zo musu.

حِكْمَةٌۢ بَـٰلِغَةٌۭ ۖ فَمَا تُغْنِ ٱلنُّذُرُ ﴿٥﴾

Hikima cikakka! Sai dai abũbuwan gargaɗi bã su amfãni.

فَتَوَلَّ عَنْهُمْ ۘ يَوْمَ يَدْعُ ٱلدَّاعِ إِلَىٰ شَىْءٍۢ نُّكُرٍ ﴿٦﴾

Sabõda haka, ka bar su! Rãnar da mai kiran zai yi kira zuwa ga wani abu abin ƙyama.

بسم الله الرحمن الرحيم Lar 20 Safar
الأربعاء 20 صفر
أحدب متناقص Cikakken Wata Raguwa Rana 21.9 / 29.5
Haske 53%
Wata Sabo a cikin kwana 8
سبحان الله وبحمده Tsarkin Allah da godiyarSa