المعارج · Juz 29
Tafi zuwa
Alamomi
Mai karantawa / Qārī
Gudun sauti
Maimaita aya
Maimaita
Gungumewa kai
Fassara

Abubakar Mahmoud Gumi

Fontin larabci
Girman rubutu
Larabci
Fassara
Zangin da za a hadda
Maimaitawa
Kowane aya
Cikakken madauki
Babban mai karantawa
A ci gaba - Madauki A-B /

Kara Surah Al-Maarij

Surah Al-Maarij (المعارج) ita ce surah na Makka ta Alkur'ani tana da ayoyi 44. Ku karanta, ku saurari kuma ku hadda wannan surah tare da kayanmu masu hulɗa.

An sabunta a 10 Yuli 2026 03h52

📖 Karatu minti 2

Surah Al-Maarij cikin lambobi

Tsarin saukarwa
Saukarwa n° 79 / 114
(na Makka)
222
kalmomi
-69.1% vs matsakaici
1,011
haruffa
-67.1% vs matsakaici
2
min karantawa
44
ayoyi
-19.6% vs matsakaici

Yawan amfani da kalmomin bincike في سورة Al-Maarij

الله 1
رب 4

Haruffa da yawa suke fitowa في سورة Al-Maarij

م
98
#1
ل
96
#2
و
83
#3
ن
80
#4
ي
63
#5
Kara Surah Al-Ma'aarij
سورة المعارج
Juz 29 33.4% (144/431)
Hizb 57 69.9% (144/206)

يُبَصَّرُونَهُمْ ۚ يَوَدُّ ٱلْمُجْرِمُ لَوْ يَفْتَدِى مِنْ عَذَابِ يَوْمِئِذٍۭ بِبَنِيهِ ﴿١١﴾

Ana sanya su, su gajũna, mai laifi na gũrin dã zai iya yin fansa, daga azãbar rãnar nan, da ɗiyansa,

وَصَـٰحِبَتِهِۦ وَأَخِيهِ ﴿١٢﴾

Da matarsa da ɗan'uwansa.

وَفَصِيلَتِهِ ٱلَّتِى تُـْٔوِيهِ ﴿١٣﴾

Da danginsa, mãsu tattarã shi.

وَمَن فِى ٱلْأَرْضِ جَمِيعًۭا ثُمَّ يُنجِيهِ ﴿١٤﴾

Da wanda ke a cikin dũniya duka gabã ɗaya, sa'an nan fansar, ta tsĩrar da shi.

كَلَّآ ۖ إِنَّهَا لَظَىٰ ﴿١٥﴾

A'aha! Lalle ne fa, ita ce Lazã,

نَزَّاعَةًۭ لِّلشَّوَىٰ ﴿١٦﴾

Mai twãle fãtar goshi.

تَدْعُوا۟ مَنْ أَدْبَرَ وَتَوَلَّىٰ ﴿١٧﴾

Tanã kiran wanda ya jũya bãya (daga addini) kuma ya kau da kai.

وَجَمَعَ فَأَوْعَىٰٓ ﴿١٨﴾

Ya tãra (dũkiya), kuma ya sanya ta a cikin jaka.

۞ إِنَّ ٱلْإِنسَـٰنَ خُلِقَ هَلُوعًا ﴿١٩﴾

Lalle ne mutum an halitta shi mai ciwon kwaɗayi.

إِذَا مَسَّهُ ٱلشَّرُّ جَزُوعًۭا ﴿٢٠﴾

Idan sharri ya shãfe shi, ya kãsa haƙuri.

وَإِذَا مَسَّهُ ٱلْخَيْرُ مَنُوعًا ﴿٢١﴾

Kuma idan alhẽri ya shãfe shi, ya yi rõwa.

إِلَّا ٱلْمُصَلِّينَ ﴿٢٢﴾

Sai mãsu yin salla,

ٱلَّذِينَ هُمْ عَلَىٰ صَلَاتِهِمْ دَآئِمُونَ ﴿٢٣﴾

Waɗanda suke, a kan sallarsu, su, mãsu dawwama ne.

وَٱلَّذِينَ فِىٓ أَمْوَٰلِهِمْ حَقٌّۭ مَّعْلُومٌۭ ﴿٢٤﴾

Kuma waɗanda a cikin dũkiyarsu, akwai wani haƙƙi sananne.

لِّلسَّآئِلِ وَٱلْمَحْرُومِ ﴿٢٥﴾

Ga (matalauci) mai rõƙo da wanda aka hanã wa roƙon.

وَٱلَّذِينَ يُصَدِّقُونَ بِيَوْمِ ٱلدِّينِ ﴿٢٦﴾

Da waɗannan da ke gaskata rãnar sakamako.

وَٱلَّذِينَ هُم مِّنْ عَذَابِ رَبِّهِم مُّشْفِقُونَ ﴿٢٧﴾

Da waɗannan sabõda azãbar Ubangijinsu, suna jin tsõro.

إِنَّ عَذَابَ رَبِّهِمْ غَيْرُ مَأْمُونٍۢ ﴿٢٨﴾

Lalle ne, azãbar Ubangijinsu bã wadda ake iya amincẽwaba ce.

وَٱلَّذِينَ هُمْ لِفُرُوجِهِمْ حَـٰفِظُونَ ﴿٢٩﴾

Da waɗanda suke, ga farjojinsu, mãsu tsarewa ne.

إِلَّا عَلَىٰٓ أَزْوَٰجِهِمْ أَوْ مَا مَلَكَتْ أَيْمَـٰنُهُمْ فَإِنَّهُمْ غَيْرُ مَلُومِينَ ﴿٣٠﴾

Sai fa a kan matan aurensu da abin da hannayensu na dãma suka mallaka. To lalle ne sũkam ba waɗanda ake zargi ba ne.

فَمَنِ ٱبْتَغَىٰ وَرَآءَ ذَٰلِكَ فَأُو۟لَـٰٓئِكَ هُمُ ٱلْعَادُونَ ﴿٣١﴾

To, duk wanda ya nẽmi abin da yake a bayan wannan, to, waɗancan sũ ne mãsu ƙetare iyãka.

وَٱلَّذِينَ هُمْ لِأَمَـٰنَـٰتِهِمْ وَعَهْدِهِمْ رَٰعُونَ ﴿٣٢﴾

Kuma da waɗannan da suke ga amãnõninsu da alkawarinsu mãsu tsarẽwa ne.

وَٱلَّذِينَ هُم بِشَهَـٰدَٰتِهِمْ قَآئِمُونَ ﴿٣٣﴾

Kuma da waɗanda suke, ga shaidarsu, mãsu dãgẽwa ne.

وَٱلَّذِينَ هُمْ عَلَىٰ صَلَاتِهِمْ يُحَافِظُونَ ﴿٣٤﴾

Kuma waɗanda suke, a kan sallarsu, mãsu tsarẽwa ne.

أُو۟لَـٰٓئِكَ فِى جَنَّـٰتٍۢ مُّكْرَمُونَ ﴿٣٥﴾

Waɗannan, a cikin gidãjen Aljanna, waɗanda ake girmamãwa ne

فَمَالِ ٱلَّذِينَ كَفَرُوا۟ قِبَلَكَ مُهْطِعِينَ ﴿٣٦﴾

Mẽ yã sãmi waɗanda suka kãfirta, a wajenka, sunã gaugãwar (gudu).

عَنِ ٱلْيَمِينِ وَعَنِ ٱلشِّمَالِ عِزِينَ ﴿٣٧﴾

Daga jihar dãma, kuma daga jihar hagu, jama'a-jama'a!

أَيَطْمَعُ كُلُّ ٱمْرِئٍۢ مِّنْهُمْ أَن يُدْخَلَ جَنَّةَ نَعِيمٍۢ ﴿٣٨﴾

Shin kõwane mutum daga cikinsu yana nẽman a shigar da shi a Aljannar ni'ima ne (ba da wani aiki ba)?

كَلَّآ ۖ إِنَّا خَلَقْنَـٰهُم مِّمَّا يَعْلَمُونَ ﴿٣٩﴾

A'aha! Lalle Mũ, Mun halitta su, daga abin da suka sani.

Kara Surah Al-Ma'aarij
سورة المعارج
Juz 29 40.1% (173/431)
Hizb 57 84.0% (173/206)

فَلَآ أُقْسِمُ بِرَبِّ ٱلْمَشَـٰرِقِ وَٱلْمَغَـٰرِبِ إِنَّا لَقَـٰدِرُونَ ﴿٤٠﴾

Sabõda haka ba sai Na yi rantsuwa da Ubangijin wurãren ɓullõwar rãna da wurãren fãɗuwarta ba, lalle Mũ, Mãsu iyãwa ne.

عَلَىٰٓ أَن نُّبَدِّلَ خَيْرًۭا مِّنْهُمْ وَمَا نَحْنُ بِمَسْبُوقِينَ ﴿٤١﴾

Ga Mu musanya waɗanda suke mafi alhẽri, daga gare su. Kuma ba Mu kasance waɗanda ake rinjãya ba.

فَذَرْهُمْ يَخُوضُوا۟ وَيَلْعَبُوا۟ حَتَّىٰ يُلَـٰقُوا۟ يَوْمَهُمُ ٱلَّذِى يُوعَدُونَ ﴿٤٢﴾

Sabõda haka ka bar su, su dulmuya, kuma su yi wãsã, har su haɗu da rãnarsu wadda ake yi musu alkawari (da ita).

يَوْمَ يَخْرُجُونَ مِنَ ٱلْأَجْدَاثِ سِرَاعًۭا كَأَنَّهُمْ إِلَىٰ نُصُبٍۢ يُوفِضُونَ ﴿٤٣﴾

Rãnar da suke fitowa daga kaburbura da gaugãwa, kamar sũ, zuwa ga wata kafaffiyar (tuta), suke yin gaugãwa.

خَـٰشِعَةً أَبْصَـٰرُهُمْ تَرْهَقُهُمْ ذِلَّةٌۭ ۚ ذَٰلِكَ ٱلْيَوْمُ ٱلَّذِى كَانُوا۟ يُوعَدُونَ ﴿٤٤﴾

Maƙaskanta ga idanunsu, wani walakanci yana rufe su. wannan shi ne yinin da suka kasance ana yi musa alkawari (a kansa.)

بسم الله الرحمن الرحيم Jum 24 Muharram
الجمعة 24 محرّم
هلال متناقص Gajimaren Raguwa Rana 25 / 29.5
Haske 21%
Wata Sabo a cikin kwana 4
الله أكبر Allah Shi ne Mafi Girma