الفجر · Juz 30
Tafi zuwa
Alamomi
Mai karantawa / Qārī
Gudun sauti
Maimaita aya
Maimaita
Gungumewa kai
Fassara

Abubakar Mahmoud Gumi

Fontin larabci
Girman rubutu
Larabci
Fassara
Zangin da za a hadda
Maimaitawa
Kowane aya
Cikakken madauki
Babban mai karantawa
A ci gaba - Madauki A-B /

Kara Surah Al-Fajr

Surah Al-Fajr (الفجر) ita ce surah na Makka ta Alkur'ani tana da ayoyi 30. Ku karanta, ku saurari kuma ku hadda wannan surah tare da kayanmu masu hulɗa.

An sabunta a 10 Yuli 2026 03h52

📖 Karatu minti 1

Surah Al-Fajr cikin lambobi

Tsarin saukarwa
Saukarwa n° 10 / 114
(na Makka)
139
kalmomi
-80.7% vs matsakaici
613
haruffa
-80.0% vs matsakaici
1
min karantawa
30
ayoyi
-45.2% vs matsakaici

Yawan amfani da kalmomin bincike في سورة Al-Fajr

الله 0
رب 8

Haruffa da yawa suke fitowa في سورة Al-Fajr

ل
66
#1
ا
47
#2
و
39
#3
م
32
#4
ٱ
31
#5
Kara Surah Al-Fajr
سورة الفجر
Juz 30 56.9% (321/564)
Hizb 60 15.6% (45/288)

وَٱلْفَجْرِ ﴿١﴾

Inã rantsuwa da alfijiri.

وَلَيَالٍ عَشْرٍۢ ﴿٢﴾

Da darũruwa gõma.

وَٱلشَّفْعِ وَٱلْوَتْرِ ﴿٣﴾

Da (adadi na) cikã da (na) mãrã.

وَٱلَّيْلِ إِذَا يَسْرِ ﴿٤﴾

Da dare idan yana shũɗewa.

هَلْ فِى ذَٰلِكَ قَسَمٌۭ لِّذِى حِجْرٍ ﴿٥﴾

Ko a cikin waɗannan akwai abin rantsuwa ga mai hankali (da yake kange shi daga zunubi)?

أَلَمْ تَرَ كَيْفَ فَعَلَ رَبُّكَ بِعَادٍ ﴿٦﴾

Ba ka ga yadda Ubangijinka Ya aikata da Ãdãwa ba?

إِرَمَ ذَاتِ ٱلْعِمَادِ ﴿٧﴾

Iramawa mãsu sakon ƙĩrar jiki.

ٱلَّتِى لَمْ يُخْلَقْ مِثْلُهَا فِى ٱلْبِلَـٰدِ ﴿٨﴾

Waɗanda ba a halitta kwatankwacinsu ba a cikin garũruwa (na dũniya).

وَثَمُودَ ٱلَّذِينَ جَابُوا۟ ٱلصَّخْرَ بِٱلْوَادِ ﴿٩﴾

Da samũdãwa waɗanda suka fasa duwãtsu a cikin Wadi suka yi gidãje)?

وَفِرْعَوْنَ ذِى ٱلْأَوْتَادِ ﴿١٠﴾

Da Fir'auna mai turãku.

ٱلَّذِينَ طَغَوْا۟ فِى ٱلْبِلَـٰدِ ﴿١١﴾

Waɗanda suka ƙẽtare iyãkarsu, a cikin garũruwa?

فَأَكْثَرُوا۟ فِيهَا ٱلْفَسَادَ ﴿١٢﴾

Sabõda haka, suka yawaita yin ɓarna a cikinsu.

فَصَبَّ عَلَيْهِمْ رَبُّكَ سَوْطَ عَذَابٍ ﴿١٣﴾

Sabõda haka Ubangijinka Ya zuba musu bũlãlar azãba.

إِنَّ رَبَّكَ لَبِٱلْمِرْصَادِ ﴿١٤﴾

Lalle ne, Ubangijinka Yana nan a mafaka.

فَأَمَّا ٱلْإِنسَـٰنُ إِذَا مَا ٱبْتَلَىٰهُ رَبُّهُۥ فَأَكْرَمَهُۥ وَنَعَّمَهُۥ فَيَقُولُ رَبِّىٓ أَكْرَمَنِ ﴿١٥﴾

To, amma fa mutum idan Ubangijibsa Ya jarraba shi, wãto Yã girmama shi kuma Ya yi masa ni'ima, sai ya ce: "Ubangijina Ya girmama ni."

وَأَمَّآ إِذَا مَا ٱبْتَلَىٰهُ فَقَدَرَ عَلَيْهِ رِزْقَهُۥ فَيَقُولُ رَبِّىٓ أَهَـٰنَنِ ﴿١٦﴾

Kuma idan Ya jarraba shi, wãto Ya ƙuntata masa abincinsa, sai ya ce: "Ubangijina Ya walãkanta ni."

كَلَّا ۖ بَل لَّا تُكْرِمُونَ ٱلْيَتِيمَ ﴿١٧﴾

A'aha! Bari wannan, ai bã ku girmama marãya!

وَلَا تَحَـٰٓضُّونَ عَلَىٰ طَعَامِ ٱلْمِسْكِينِ ﴿١٨﴾

Bã ku kwaɗaitã wa jũnanku ga (tattalin) abincin matalauci!

وَتَأْكُلُونَ ٱلتُّرَاثَ أَكْلًۭا لَّمًّۭا ﴿١٩﴾

Kuma kuna cin dũkiyar gãdo, ci na tãrãwa.

وَتُحِبُّونَ ٱلْمَالَ حُبًّۭا جَمًّۭا ﴿٢٠﴾

Kuma kuna son dũkiya, so mai yawa.

كَلَّآ إِذَا دُكَّتِ ٱلْأَرْضُ دَكًّۭا دَكًّۭا ﴿٢١﴾

A'aha! Idan aka niƙa ƙasa niƙewa sosai.

وَجَآءَ رَبُّكَ وَٱلْمَلَكُ صَفًّۭا صَفًّۭا ﴿٢٢﴾

Kuma Ubangijinka Ya zo, alhãli malã'iku na jẽre, safũ- safu.

وَجِا۟ىٓءَ يَوْمَئِذٍۭ بِجَهَنَّمَ ۚ يَوْمَئِذٍۢ يَتَذَكَّرُ ٱلْإِنسَـٰنُ وَأَنَّىٰ لَهُ ٱلذِّكْرَىٰ ﴿٢٣﴾

Kuma a ranar nan aka zo da Jahannama. A ranar nan mutum zai yi tunãni. To, inã fa tunãni yake a gare shi!

Kara Surah Al-Fajr
سورة الفجر
Juz 30 61.0% (344/564)
Hizb 60 23.6% (68/288)

يَقُولُ يَـٰلَيْتَنِى قَدَّمْتُ لِحَيَاتِى ﴿٢٤﴾

Yana dinga cẽwa, "Kaitona, dã na gabatar (da aikin ƙwarai) domin rãyuwata!"

فَيَوْمَئِذٍۢ لَّا يُعَذِّبُ عَذَابَهُۥٓ أَحَدٌۭ ﴿٢٥﴾

To, a rãnar nan bãbu wani mai yin azãba irin azãbar Allah.

وَلَا يُوثِقُ وَثَاقَهُۥٓ أَحَدٌۭ ﴿٢٦﴾

Kuma bãbu wani mai ɗauri irin ɗaurinSa.

يَـٰٓأَيَّتُهَا ٱلنَّفْسُ ٱلْمُطْمَئِنَّةُ ﴿٢٧﴾

Yã kai rai mai natsuwa!

ٱرْجِعِىٓ إِلَىٰ رَبِّكِ رَاضِيَةًۭ مَّرْضِيَّةًۭ ﴿٢٨﴾

Ka koma zuwa ga Ubangijinka, alhãli kana mai yarda (da abin da Ya ƙaddara maka a dũniya) abar yardarwa (da sakamakon da zã a ba ka a Lãhira).

فَٱدْخُلِى فِى عِبَـٰدِى ﴿٢٩﴾

Sabõbda haka, ka shiga cikin bãyiNa (mãsu bin umurui a dũniya).

وَٱدْخُلِى جَنَّتِى ﴿٣٠﴾

Kuma ka shiga AljannaTa (a Lãhira).

بسم الله الرحمن الرحيم Jum 24 Muharram
الجمعة 24 محرّم
هلال متناقص Gajimaren Raguwa Rana 25.1 / 29.5
Haske 21%
Wata Sabo a cikin kwana 4
الحمد لله Alhamdulillah - Godiya ta tabbata ga Allah