الشمس · Juz 30
Tafi zuwa
Alamomi
Mai karantawa / Qārī
Gudun sauti
Maimaita aya
Maimaita
Gungumewa kai
Fassara

Abubakar Mahmoud Gumi

Fontin larabci
Girman rubutu
Larabci
Fassara
Zangin da za a hadda
Maimaitawa
Kowane aya
Cikakken madauki
Babban mai karantawa
A ci gaba - Madauki A-B /

Kara Surah Ash-Shams

Surah Ash-Shams (الشمس) ita ce surah na Makka ta Alkur'ani tana da ayoyi 15. Ku karanta, ku saurari kuma ku hadda wannan surah tare da kayanmu masu hulɗa.

An sabunta a 10 Yuli 2026 03h52

📖 Karatu minti 1

Surah Ash-Shams cikin lambobi

Tsarin saukarwa
Saukarwa n° 26 / 114
(na Makka)
54
kalmomi
-92.5% vs matsakaici
255
haruffa
-91.7% vs matsakaici
1
min karantawa
15
ayoyi
-72.6% vs matsakaici

Yawan amfani da kalmomin bincike في سورة Ash-Shams

الله 2
رب 1

Haruffa da yawa suke fitowa في سورة Ash-Shams

ا
31
#1
ه
27
#2
و
24
#3
ل
20
#4
م
16
#5
Kara Surah Ash-Shams
سورة الشمس
Juz 30 65.8% (371/564)
Hizb 60 33.0% (95/288)

وَٱلشَّمْسِ وَضُحَىٰهَا ﴿١﴾

Ina rantsuwa da rãnã da hantsinta.

وَٱلْقَمَرِ إِذَا تَلَىٰهَا ﴿٢﴾

Kuma da wata idan ya bi ta.

وَٱلنَّهَارِ إِذَا جَلَّىٰهَا ﴿٣﴾

Da yini a lõkacin da ya bayyana ta.

وَٱلَّيْلِ إِذَا يَغْشَىٰهَا ﴿٤﴾

Da dare a lõkacin da ya ke rufe ta.

وَٱلسَّمَآءِ وَمَا بَنَىٰهَا ﴿٥﴾

Da sama da abin da ya gina ta.

وَٱلْأَرْضِ وَمَا طَحَىٰهَا ﴿٦﴾

Da ƙasã da abin da ya shimfiɗa ta.

وَنَفْسٍۢ وَمَا سَوَّىٰهَا ﴿٧﴾

Da rai da abin da ya daidaita shi.

فَأَلْهَمَهَا فُجُورَهَا وَتَقْوَىٰهَا ﴿٨﴾

Sa'an nan ya sanar da shi fãjircinsa da shiryuwarsa.

قَدْ أَفْلَحَ مَن زَكَّىٰهَا ﴿٩﴾

Lalle ne wanda ya tsarkake shi (rai) ya sãmi babban rabo.

وَقَدْ خَابَ مَن دَسَّىٰهَا ﴿١٠﴾

Kuma lalle ne wanda ya turbuɗe shi (da laifi) ya tãɓe.

كَذَّبَتْ ثَمُودُ بِطَغْوَىٰهَآ ﴿١١﴾

Samũdãwa sun ƙaryata (Annabinsu), dõmin girman kansu.

إِذِ ٱنۢبَعَثَ أَشْقَىٰهَا ﴿١٢﴾

A lõkacin da mafi shaƙãwarsu ya tafi (wurin sõke rãkumar sãlihu).

فَقَالَ لَهُمْ رَسُولُ ٱللَّهِ نَاقَةَ ٱللَّهِ وَسُقْيَـٰهَا ﴿١٣﴾

Sai Manzon Allah ya gaya musu cewa: "Ina tsõratar da ku ga rãƙumar Allah da ruwan shanta!"

فَكَذَّبُوهُ فَعَقَرُوهَا فَدَمْدَمَ عَلَيْهِمْ رَبُّهُم بِذَنۢبِهِمْ فَسَوَّىٰهَا ﴿١٤﴾

Sai suka ƙaryata shi, sa'an nan suka sõke ta. Sabõda haka Ubangijinsu Ya darkãke su, sabõda zunubinsu. Sa'an nan Ya daidaita ta (azãbar ga mai laifi da maras laifi).

وَلَا يَخَافُ عُقْبَـٰهَا ﴿١٥﴾

Kuma bã ya tsõron ãƙibarta (ita halakãwar).

بسم الله الرحمن الرحيم Jum 24 Muharram
الجمعة 24 محرّم
هلال متناقص Gajimaren Raguwa Rana 25 / 29.5
Haske 21%
Wata Sabo a cikin kwana 4
لا حول ولا قوة إلا بالله Babu wata ƙarfi ko iko sai na Allah