Abubakar Mahmoud Gumi
Shafi 568 na Mushaf yana ɗauke da ayoyi 28. Yana cikin Juz 29, Hizb 57.
An sabunta a 10 Yuli 2026 03h52
coran.read_full_page : Kara Shafi 568 na Alkur'ani →
فَلَيْسَ لَهُ ٱلْيَوْمَ هَـٰهُنَا حَمِيمٌۭ ﴿٣٥﴾
"Sabõda haka, a yau, a nan, bã ya da masõyi."
وَلَا طَعَامٌ إِلَّا مِنْ غِسْلِينٍۢ ﴿٣٦﴾
"Kuma bãbu wani abinci, sai daga (itãcen) gislĩn."
لَّا يَأْكُلُهُۥٓ إِلَّا ٱلْخَـٰطِـُٔونَ ﴿٣٧﴾
"Bãbu mai cin sa sai mãsu ganganci."
فَلَآ أُقْسِمُ بِمَا تُبْصِرُونَ ﴿٣٨﴾
To, ba sai Nã yi rantsuwa da abin da kuke iya gani ba,
وَمَا لَا تُبْصِرُونَ ﴿٣٩﴾
Da abin da bã ku iya gani.
إِنَّهُۥ لَقَوْلُ رَسُولٍۢ كَرِيمٍۢ ﴿٤٠﴾
Lalle ne, shi (Alƙur'ani) tabbas maganar wani manzo (Jibirilu) mai daraja ne.
وَمَا هُوَ بِقَوْلِ شَاعِرٍۢ ۚ قَلِيلًۭا مَّا تُؤْمِنُونَ ﴿٤١﴾
Kuma shi ba maganar wani mawãƙi ba ne. Kaɗan ƙwarai zã ku gaskata.
وَلَا بِقَوْلِ كَاهِنٍۢ ۚ قَلِيلًۭا مَّا تَذَكَّرُونَ ﴿٤٢﴾
Kuma bã maganar bõka ba ne. Kaɗan ƙwarai zã ku iya tunãwa.
تَنزِيلٌۭ مِّن رَّبِّ ٱلْعَـٰلَمِينَ ﴿٤٣﴾
Abin saukarwã ne daga Ubangijin halitta duka.
وَلَوْ تَقَوَّلَ عَلَيْنَا بَعْضَ ٱلْأَقَاوِيلِ ﴿٤٤﴾
Kuma dã (Muhammadu) yã faɗi wata maganã, yã jingina ta garẽ Mu.
لَأَخَذْنَا مِنْهُ بِٱلْيَمِينِ ﴿٤٥﴾
Dã Mun kãma shi da dãma.
ثُمَّ لَقَطَعْنَا مِنْهُ ٱلْوَتِينَ ﴿٤٦﴾
sa'an nan, lalle ne, dã Mun kãtse masa lakã.
فَمَا مِنكُم مِّنْ أَحَدٍ عَنْهُ حَـٰجِزِينَ ﴿٤٧﴾
Kuma daga cikinku bãbu wasu mãsu iya kãre (azãbarMu) daga gare shi.
وَإِنَّهُۥ لَتَذْكِرَةٌۭ لِّلْمُتَّقِينَ ﴿٤٨﴾
Kuma lalle ne shi (Alƙur'ãni) tanãtarwa ce ga mãsu taƙawa.
وَإِنَّا لَنَعْلَمُ أَنَّ مِنكُم مُّكَذِّبِينَ ﴿٤٩﴾
Kuma lalle, ne Mũ, wallahi Munã sane da cẽwa daga cikinku alwwai mãsu ƙaryatãwa.
وَإِنَّهُۥ لَحَسْرَةٌ عَلَى ٱلْكَـٰفِرِينَ ﴿٥٠﴾
Kuma lalle ne shi (Alƙarãni) wallahi baƙin ciki ne ga kãfirai.
وَإِنَّهُۥ لَحَقُّ ٱلْيَقِينِ ﴿٥١﴾
Kuma lalle, ne shi gaskiya ce ta yaƙshẽni.
فَسَبِّحْ بِٱسْمِ رَبِّكَ ٱلْعَظِيمِ ﴿٥٢﴾
Sabõda haka, ka tsarkake sũnan Ubangjinka, mai girma.
سَأَلَ سَآئِلٌۢ بِعَذَابٍۢ وَاقِعٍۢ ﴿١﴾
Wani mai tambaya yã yi tambaya game da azãba, mai aukuwa.
لِّلْكَـٰفِرِينَ لَيْسَ لَهُۥ دَافِعٌۭ ﴿٢﴾
Ga kãfirai, bã ta da mai tunkuɗẽwa.
مِّنَ ٱللَّهِ ذِى ٱلْمَعَارِجِ ﴿٣﴾
Daga Allah Mai matãkala.
تَعْرُجُ ٱلْمَلَـٰٓئِكَةُ وَٱلرُّوحُ إِلَيْهِ فِى يَوْمٍۢ كَانَ مِقْدَارُهُۥ خَمْسِينَ أَلْفَ سَنَةٍۢ ﴿٤﴾
Malã'iku da Ruhi (Jibrila) sunã tãkãwa zuwa gare Shi, a cikin yini wanda gwargwadonsa, shẽkara dubu hamsin ne.
فَٱصْبِرْ صَبْرًۭا جَمِيلًا ﴿٥﴾
Sabõda haka, ka yi haƙuri, haƙuri mai kyãwo.
إِنَّهُمْ يَرَوْنَهُۥ بَعِيدًۭا ﴿٦﴾
Lalle ne su, sunã ganin ta mai nĩsa.
وَنَرَىٰهُ قَرِيبًۭا ﴿٧﴾
Kuma Mu, Muna ganin ta a kusa.
يَوْمَ تَكُونُ ٱلسَّمَآءُ كَٱلْمُهْلِ ﴿٨﴾
Rãnar da sama zã ta kasance kamar narkakkar azurfa.
وَتَكُونُ ٱلْجِبَالُ كَٱلْعِهْنِ ﴿٩﴾
Kuma duwãtsu su zama kamar saɓin sũfi.
وَلَا يَسْـَٔلُ حَمِيمٌ حَمِيمًۭا ﴿١٠﴾
Kuma abõki bã ya tambayar inda wani abõki yake.