التكوير · Juz 30
Tafi zuwa
Alamomi
Mai karantawa / Qārī
Gudun sauti
Maimaita aya
Maimaita
Gungumewa kai
Fassara

Abubakar Mahmoud Gumi

Fontin larabci
Girman rubutu
Larabci
Fassara
Zangin da za a hadda
Maimaitawa
Kowane aya
Cikakken madauki
Babban mai karantawa
A ci gaba - Madauki A-B /

Kara Shafi 586 na Alkur'ani

Shafi 586 na Mushaf yana ɗauke da ayoyi 29. Yana cikin Juz 30, Hizb 59.

An sabunta a 10 Yuli 2026 03h52

Page 586 dans le Coran

29
ayoyi
30
Juz
59
Hizb
1
Surah

Sourate dans la page 586

Juz 30
Shafi 586
سورة التكوير
Juz 30 22.7% (128/564)
Hizb 59 46.4% (128/276)

إِذَا ٱلشَّمْسُ كُوِّرَتْ ﴿١﴾

Idan rãna aka shafe haskenta

وَإِذَا ٱلنُّجُومُ ٱنكَدَرَتْ ﴿٢﴾

Kuma idan taurãri suka gurɓãce (wani ya shiga a cikin wani).

وَإِذَا ٱلْجِبَالُ سُيِّرَتْ ﴿٣﴾

Kuma idan duwãtsu aka tafiyar da su.

وَإِذَا ٱلْعِشَارُ عُطِّلَتْ ﴿٤﴾

Kuma idan rãƙuma mãsu cikunna aka sakẽ su wãwai, bã ga kõwa ba.

وَإِذَا ٱلْوُحُوشُ حُشِرَتْ ﴿٥﴾

Kuma idan dabbõbin dãji aka tattara su.

وَإِذَا ٱلْبِحَارُ سُجِّرَتْ ﴿٦﴾

Kuma idan tẽkuna aka mayar da su wuta.

وَإِذَا ٱلنُّفُوسُ زُوِّجَتْ ﴿٧﴾

Kuma idan rãyuka aka haɗa su da jikunkunansu.

وَإِذَا ٱلْمَوْءُۥدَةُ سُئِلَتْ ﴿٨﴾

Kuma idan wadda aka turbuɗe ta da rai aka tambaye ta.

بِأَىِّ ذَنۢبٍۢ قُتِلَتْ ﴿٩﴾

"Sabõda wane laifi ne aka kashe ta?"

وَإِذَا ٱلصُّحُفُ نُشِرَتْ ﴿١٠﴾

Idan takardun ayyuka aka wãtsa su (ga mãsu su).

وَإِذَا ٱلسَّمَآءُ كُشِطَتْ ﴿١١﴾

Kuma idan sama aka fẽɗe ta.

وَإِذَا ٱلْجَحِيمُ سُعِّرَتْ ﴿١٢﴾

Kuma idan Jahĩm aka hũra ta

وَإِذَا ٱلْجَنَّةُ أُزْلِفَتْ ﴿١٣﴾

Kuma idan Aljanna aka kusantar da ita.

عَلِمَتْ نَفْسٌۭ مَّآ أَحْضَرَتْ ﴿١٤﴾

Rai ya san abin da ya halartar (a rãnar nan).

فَلَآ أُقْسِمُ بِٱلْخُنَّسِ ﴿١٥﴾

To, ba sai Na yi rantsuwa da taurãri matafã ba.

ٱلْجَوَارِ ٱلْكُنَّسِ ﴿١٦﴾

Mãsu gudu suna ɓũya.

وَٱلَّيْلِ إِذَا عَسْعَسَ ﴿١٧﴾

Da dare idan ya bãyar da bãya.

وَٱلصُّبْحِ إِذَا تَنَفَّسَ ﴿١٨﴾

Da sãfiya idan ta yi lumfashi.

إِنَّهُۥ لَقَوْلُ رَسُولٍۢ كَرِيمٍۢ ﴿١٩﴾

Lalle ne shi (Alƙur'ãni) haƙƙan, maganar wani manzon (Allah) ne mai girma ga Allah.

ذِى قُوَّةٍ عِندَ ذِى ٱلْعَرْشِ مَكِينٍۢ ﴿٢٠﴾

Mai ƙarfi, mai daraja a wurin Mai Al'arshi.

مُّطَاعٍۢ ثَمَّ أَمِينٍۢ ﴿٢١﴾

Wanda ake yi wa ɗã'a (wato shugaban malã'iku) ne a can, amintacce.

وَمَا صَاحِبُكُم بِمَجْنُونٍۢ ﴿٢٢﴾

Kuma abokinku ba mahaukaci ba ne.

وَلَقَدْ رَءَاهُ بِٱلْأُفُقِ ٱلْمُبِينِ ﴿٢٣﴾

Kuma lalle ne, yã gan shi a cikin sararin sama mabayyani.

وَمَا هُوَ عَلَى ٱلْغَيْبِ بِضَنِينٍۢ ﴿٢٤﴾

Kuma shi, ga gaibi bã mai rowa ba ne.

وَمَا هُوَ بِقَوْلِ شَيْطَـٰنٍۢ رَّجِيمٍۢ ﴿٢٥﴾

Kuma shi (Alƙur'ani) bã maganar shaiɗani, wanda aka la'ana, ba ce.

فَأَيْنَ تَذْهَبُونَ ﴿٢٦﴾

Shin, a inã zã ku tafi?

إِنْ هُوَ إِلَّا ذِكْرٌۭ لِّلْعَـٰلَمِينَ ﴿٢٧﴾

Lalle ne shi (Alƙur'ãni), bã kõme ba ne fãce gargaɗi ga talikai.

لِمَن شَآءَ مِنكُمْ أَن يَسْتَقِيمَ ﴿٢٨﴾

Ga wanda ya so, daga cikinku, ya shiryu.

وَمَا تَشَآءُونَ إِلَّآ أَن يَشَآءَ ٱللَّهُ رَبُّ ٱلْعَـٰلَمِينَ ﴿٢٩﴾

Kuma bã zã ku so ba sai idan Allah Ubangijin halitta Yã yarda.

بسم الله الرحمن الرحيم Jum 24 Muharram
الجمعة 24 محرّم
هلال متناقص Gajimaren Raguwa Rana 25.1 / 29.5
Haske 20%
Wata Sabo a cikin kwana 4
لا إله إلا الله Babu abin bautawa sai Allah