المطففين · Juz 30
Tafi zuwa
Alamomi
Mai karantawa / Qārī
Gudun sauti
Maimaita aya
Maimaita
Gungumewa kai
Fassara

Abubakar Mahmoud Gumi

Fontin larabci
Girman rubutu
Larabci
Fassara
Zangin da za a hadda
Maimaitawa
Kowane aya
Cikakken madauki
Babban mai karantawa
A ci gaba - Madauki A-B /

Kara Shafi 588 na Alkur'ani

Shafi 588 na Mushaf yana ɗauke da ayoyi 28. Yana cikin Juz 30, Hizb 59.

An sabunta a 10 Yuli 2026 03h52

Page 588 dans le Coran

28
ayoyi
30
Juz
59
Hizb
1
Surah
Juz 30
Shafi 588
سورة المطففين
Juz 30 32.3% (182/564)
Hizb 59 65.9% (182/276)

كَلَّآ إِنَّ كِتَـٰبَ ٱلْفُجَّارِ لَفِى سِجِّينٍۢ ﴿٧﴾

Haƙĩƙa lalle ne littãfin fãjirai dãhir, yana a cikin Sijjĩn.

وَمَآ أَدْرَىٰكَ مَا سِجِّينٌۭ ﴿٨﴾

Kuma, mẽ ya sanar da kai abin da akẽ cẽ wa Sijjĩn?

كِتَـٰبٌۭ مَّرْقُومٌۭ ﴿٩﴾

Wani 1ittãfi ne rubũtacce.

وَيْلٌۭ يَوْمَئِذٍۢ لِّلْمُكَذِّبِينَ ﴿١٠﴾

Bone yã tabbata a rãnar nan ga mãsu ƙaryatãwa.

ٱلَّذِينَ يُكَذِّبُونَ بِيَوْمِ ٱلدِّينِ ﴿١١﴾

Waɗanda suke ƙaryatãwa game da rãnar sakamako.

وَمَا يُكَذِّبُ بِهِۦٓ إِلَّا كُلُّ مُعْتَدٍ أَثِيمٍ ﴿١٢﴾

Babũ mai ƙaryatãwa gare shi fãce dukan mai ƙẽtare haddi mai yawan zunubi.

إِذَا تُتْلَىٰ عَلَيْهِ ءَايَـٰتُنَا قَالَ أَسَـٰطِيرُ ٱلْأَوَّلِينَ ﴿١٣﴾

Idan ana karãtun ãyõyinmu, a kansa, sai ya ce: tãtsũniyõyin mutãnen farko ne.

كَلَّا ۖ بَلْ ۜ رَانَ عَلَىٰ قُلُوبِهِم مَّا كَانُوا۟ يَكْسِبُونَ ﴿١٤﴾

A'aha! Bã haka ba, abin da suka kasance suna aikatãwa dai, yã yi tsãtsa a cikin zukãtãnsu.

كَلَّآ إِنَّهُمْ عَن رَّبِّهِمْ يَوْمَئِذٍۢ لَّمَحْجُوبُونَ ﴿١٥﴾

A'aha! Haƙĩƙa, lalle ne sũ daga Ubangijinsu, rãnar nan, waɗanda ake shãmakancẽwa ne.

ثُمَّ إِنَّهُمْ لَصَالُوا۟ ٱلْجَحِيمِ ﴿١٦﴾

Sa'an nan, lalle ne, sũ mãsu shiga cikin Jahĩm ne.

ثُمَّ يُقَالُ هَـٰذَا ٱلَّذِى كُنتُم بِهِۦ تُكَذِّبُونَ ﴿١٧﴾

Sa'an nan a ce: "Wannan shi ne abin da kuka kasance kuna ƙaryatãwa game da shi."

كَلَّآ إِنَّ كِتَـٰبَ ٱلْأَبْرَارِ لَفِى عِلِّيِّينَ ﴿١٨﴾

A'aha! Haƙĩƙa lalle ne littãfin mãsu ɗã'ã yana a cikin Illiyyĩna?

وَمَآ أَدْرَىٰكَ مَا عِلِّيُّونَ ﴿١٩﴾

Kuma mẽne ne yã sanar da kai abin da ake cẽwa Illiyyũna?

كِتَـٰبٌۭ مَّرْقُومٌۭ ﴿٢٠﴾

Wani littãfi ne rubũtacce.

يَشْهَدُهُ ٱلْمُقَرَّبُونَ ﴿٢١﴾

Muƙarrabai suke halarta shi.

إِنَّ ٱلْأَبْرَارَ لَفِى نَعِيمٍ ﴿٢٢﴾

Lalle ne, mãsu ɗã'ã ga Allah tabbas suna cikin ni'ima.

عَلَى ٱلْأَرَآئِكِ يَنظُرُونَ ﴿٢٣﴾

A kan karagu, suna ta kallo.

تَعْرِفُ فِى وُجُوهِهِمْ نَضْرَةَ ٱلنَّعِيمِ ﴿٢٤﴾

Kana sani a cikin huskõkinsu, akwai kwarjinin ni'ima.

يُسْقَوْنَ مِن رَّحِيقٍۢ مَّخْتُومٍ ﴿٢٥﴾

Ana shãyar da sũ daga wata giya wadda aka yunƙe a kan rufinta.

خِتَـٰمُهُۥ مِسْكٌۭ ۚ وَفِى ذَٰلِكَ فَلْيَتَنَافَسِ ٱلْمُتَنَـٰفِسُونَ ﴿٢٦﴾

¡arshen kurɓinta miski ne. To, a cikin wannan, mãsu gwagwarmaya su yi ta gwagwarmayar nẽma.

وَمِزَاجُهُۥ مِن تَسْنِيمٍ ﴿٢٧﴾

Kuma abin da ake gauraya ta da shi, daga tasnĩm yake.

عَيْنًۭا يَشْرَبُ بِهَا ٱلْمُقَرَّبُونَ ﴿٢٨﴾

(Wato) wani marmaro ne wanda muƙarrabai ke sha daga gare shi.

إِنَّ ٱلَّذِينَ أَجْرَمُوا۟ كَانُوا۟ مِنَ ٱلَّذِينَ ءَامَنُوا۟ يَضْحَكُونَ ﴿٢٩﴾

Lalle ne, waɗanda suka kãfirta sun kasance (a dũniya) suna yi wa waɗanda suka yi ĩmãni dãriya.

وَإِذَا مَرُّوا۟ بِهِمْ يَتَغَامَزُونَ ﴿٣٠﴾

Kuma idan sun shuɗe su sai su dinga yin zunɗe.

وَإِذَا ٱنقَلَبُوٓا۟ إِلَىٰٓ أَهْلِهِمُ ٱنقَلَبُوا۟ فَكِهِينَ ﴿٣١﴾

Kuma idan suka jũya zuwa ga iyãlansu, sai su tafi suna kãkãci.

وَإِذَا رَأَوْهُمْ قَالُوٓا۟ إِنَّ هَـٰٓؤُلَآءِ لَضَآلُّونَ ﴿٣٢﴾

Kuma idan sun gan su sai su ce: "Lalle waɗannan ɓatattu ne."

وَمَآ أُرْسِلُوا۟ عَلَيْهِمْ حَـٰفِظِينَ ﴿٣٣﴾

Alhãli kuwa, ba a aike su ba dõmin su zama mãsu tsaro a kansu.

فَٱلْيَوْمَ ٱلَّذِينَ ءَامَنُوا۟ مِنَ ٱلْكُفَّارِ يَضْحَكُونَ ﴿٣٤﴾

To, yau fa (a Lãhira] waɗanda suka yi ĩmãni, sũ ke yi wa kãfirai dãriya.

بسم الله الرحمن الرحيم Jum 24 Muharram
الجمعة 24 محرّم
هلال متناقص Gajimaren Raguwa Rana 25 / 29.5
Haske 21%
Wata Sabo a cikin kwana 4
حسبنا الله ونعم الوكيل Allah Ya isa mana, Shi ne mafi kyawun Mai Kiyaye