المطففين · Juz 30
Tafi zuwa
Alamomi
Mai karantawa / Qārī
Gudun sauti
Maimaita aya
Maimaita
Gungumewa kai
Fassara

Abubakar Mahmoud Gumi

Fontin larabci
Girman rubutu
Larabci
Fassara
Zangin da za a hadda
Maimaitawa
Kowane aya
Cikakken madauki
Babban mai karantawa
A ci gaba - Madauki A-B /

Kara Shafi 589 na Alkur'ani

Shafi 589 na Mushaf yana ɗauke da ayoyi 27. Yana cikin Juz 30, Hizb 59.

An sabunta a 10 Yuli 2026 03h52

Page 589 dans le Coran

27
ayoyi
30
Juz
59
Hizb
2
Surah
Juz 30
Shafi 589
سورة المطففين
Juz 30 37.2% (210/564)
Hizb 59 76.1% (210/276)

عَلَى ٱلْأَرَآئِكِ يَنظُرُونَ ﴿٣٥﴾

A kan karagu, suna ta kallo.

هَلْ ثُوِّبَ ٱلْكُفَّارُ مَا كَانُوا۟ يَفْعَلُونَ ﴿٣٦﴾

Shin an sãka ma kãfirai abin da suka kasance suna aikatawa?

إِذَا ٱلسَّمَآءُ ٱنشَقَّتْ ﴿١﴾

Idan sama ta kẽce,

وَأَذِنَتْ لِرَبِّهَا وَحُقَّتْ ﴿٢﴾

Ta saurari Ubangijinta, kuma aka wajabta mata yin saurãron,

وَإِذَا ٱلْأَرْضُ مُدَّتْ ﴿٣﴾

Kuma idan ƙasã aka mĩƙe ta,

وَأَلْقَتْ مَا فِيهَا وَتَخَلَّتْ ﴿٤﴾

Kuma ta jẽfar da abin da yake a cikinta, tã wõfinta daga kõme.

وَأَذِنَتْ لِرَبِّهَا وَحُقَّتْ ﴿٥﴾

Kuma ta saurãri Ubangijinta, aka wajabta mata yin saurãren,

يَـٰٓأَيُّهَا ٱلْإِنسَـٰنُ إِنَّكَ كَادِحٌ إِلَىٰ رَبِّكَ كَدْحًۭا فَمُلَـٰقِيهِ ﴿٦﴾

Ya kai mutum! Lalle ne kai mai aikin wahal da kai ne zuwa ga Ubangijinka, wahala mai tsanani, To, kai mai haɗuwa da Shi ne.

فَأَمَّا مَنْ أُوتِىَ كِتَـٰبَهُۥ بِيَمِينِهِۦ ﴿٧﴾

To, amma wanda aka bai wa littãfinsa da damansa.

فَسَوْفَ يُحَاسَبُ حِسَابًۭا يَسِيرًۭا ﴿٨﴾

To, za a yi masa hisãbi, hisãbi mai sauƙi.

وَيَنقَلِبُ إِلَىٰٓ أَهْلِهِۦ مَسْرُورًۭا ﴿٩﴾

Kuma ya jũya zuwa ga iyãlinsa (a cikin Aljanna), yanã mai raha.

وَأَمَّا مَنْ أُوتِىَ كِتَـٰبَهُۥ وَرَآءَ ظَهْرِهِۦ ﴿١٠﴾

Kuma amma wanda aka bai wa littãfinsa, daga wajen bãyansa.

فَسَوْفَ يَدْعُوا۟ ثُبُورًۭا ﴿١١﴾

To, zã shi dinga kiran halaka!

وَيَصْلَىٰ سَعِيرًا ﴿١٢﴾

Kuma ya shiga sa'ĩr.

إِنَّهُۥ كَانَ فِىٓ أَهْلِهِۦ مَسْرُورًا ﴿١٣﴾

Lal1e ne shi, yã kasance (a dũniya) cikin iyãlinsa yanã mai raha.

إِنَّهُۥ ظَنَّ أَن لَّن يَحُورَ ﴿١٤﴾

Lalle ne yã yi zaton bã zai kõmo ba.

بَلَىٰٓ إِنَّ رَبَّهُۥ كَانَ بِهِۦ بَصِيرًۭا ﴿١٥﴾

Na'am! Lalle ne, Ubangijinsa Ya kasance Mai gani gare shi.

فَلَآ أُقْسِمُ بِٱلشَّفَقِ ﴿١٦﴾

To, ba sai Nã rantse da shafaƙi ba.

وَٱلَّيْلِ وَمَا وَسَقَ ﴿١٧﴾

Da dare, da abin da ya ƙunsa.

وَٱلْقَمَرِ إِذَا ٱتَّسَقَ ﴿١٨﴾

Da watã idan (haskensa) ya cika.

لَتَرْكَبُنَّ طَبَقًا عَن طَبَقٍۢ ﴿١٩﴾

Lalle ne kunã hawan wani hãli daga wani hãli.

فَمَا لَهُمْ لَا يُؤْمِنُونَ ﴿٢٠﴾

To, mẽ ya sãme su, ba su yin ĩmãni?

وَإِذَا قُرِئَ عَلَيْهِمُ ٱلْقُرْءَانُ لَا يَسْجُدُونَ ۩ ﴿٢١﴾

Kuma idan an karanta Alkur'ãni a kansu, bã su yin tawãli'u?

بَلِ ٱلَّذِينَ كَفَرُوا۟ يُكَذِّبُونَ ﴿٢٢﴾

Ba haka ba! waɗanda suka kãfirta, sai ƙaryatãwa suke yi.

وَٱللَّهُ أَعْلَمُ بِمَا يُوعُونَ ﴿٢٣﴾

Alhãli Allah Shĩ ne Mafi sani ga abin a suke tãrãwa.

فَبَشِّرْهُم بِعَذَابٍ أَلِيمٍ ﴿٢٤﴾

Saboda haka, ka yi musu bushãra da azãba mai raɗaɗi.

إِلَّا ٱلَّذِينَ ءَامَنُوا۟ وَعَمِلُوا۟ ٱلصَّـٰلِحَـٰتِ لَهُمْ أَجْرٌ غَيْرُ مَمْنُونٍۭ ﴿٢٥﴾

Fãce waɗanda suka yi ĩmãni, suka aikata ayyukan ƙwarai, sunã da wani sakamako wanda bã ya yankẽwa.

بسم الله الرحمن الرحيم Jum 24 Muharram
الجمعة 24 محرّم
هلال متناقص Gajimaren Raguwa Rana 25.1 / 29.5
Haske 21%
Wata Sabo a cikin kwana 4
حسبنا الله ونعم الوكيل Allah Ya isa mana, Shi ne mafi kyawun Mai Kiyaye