الليل · Juz 30
Tafi zuwa
Alamomi
Mai karantawa / Qārī
Gudun sauti
Maimaita aya
Maimaita
Gungumewa kai
Fassara

Abubakar Mahmoud Gumi

Fontin larabci
Girman rubutu
Larabci
Fassara
Zangin da za a hadda
Maimaitawa
Kowane aya
Cikakken madauki
Babban mai karantawa
A ci gaba - Madauki A-B /

Kara Shafi 596 na Alkur'ani

Shafi 596 na Mushaf yana ɗauke da ayoyi 26. Yana cikin Juz 30, Hizb 60.

An sabunta a 10 Yuli 2026 03h52

Page 596 dans le Coran

26
ayoyi
30
Juz
60
Hizb
3
Surah
Juz 30
Shafi 596
سورة الليل
Juz 30 70.9% (400/564)
Hizb 60 43.1% (124/288)

لَا يَصْلَىٰهَآ إِلَّا ٱلْأَشْقَى ﴿١٥﴾

Bãbu mai shigarta sai mafi shaƙãwa.

ٱلَّذِى كَذَّبَ وَتَوَلَّىٰ ﴿١٦﴾

Wanda ya ƙaryata, kuma ya jũya bãya.

وَسَيُجَنَّبُهَا ٱلْأَتْقَى ﴿١٧﴾

Kuma mafi taƙawa zai nisance ta.

ٱلَّذِى يُؤْتِى مَالَهُۥ يَتَزَكَّىٰ ﴿١٨﴾

Wanda yake bãyar da dũkiyarsa, alhãli yana tsarkaka.

وَمَا لِأَحَدٍ عِندَهُۥ مِن نِّعْمَةٍۢ تُجْزَىٰٓ ﴿١٩﴾

Alhãli bãbu wani mai wata ni'ima wurinsa wadda ake nẽman sakamakonta.

إِلَّا ٱبْتِغَآءَ وَجْهِ رَبِّهِ ٱلْأَعْلَىٰ ﴿٢٠﴾

Fãce dai nẽman yardar Ubangijinsa Mafi ɗaukaka.

وَلَسَوْفَ يَرْضَىٰ ﴿٢١﴾

To, lalle ne zai yarda (da sakamakon da zã a bã shi).

وَٱلضُّحَىٰ ﴿١﴾

Inã rantsuwa da hantsi.

وَٱلَّيْلِ إِذَا سَجَىٰ ﴿٢﴾

Da dare a lõkacin da ya rufe (da duhunsa).

مَا وَدَّعَكَ رَبُّكَ وَمَا قَلَىٰ ﴿٣﴾

Ubangijinka bai yi maka bankwana ba, kuma bai ƙĩ kaba.

وَلَلْـَٔاخِرَةُ خَيْرٌۭ لَّكَ مِنَ ٱلْأُولَىٰ ﴿٤﴾

Kuma lalle ta ƙarshe ce mafi alheri a gare ka daga ta farko.

وَلَسَوْفَ يُعْطِيكَ رَبُّكَ فَتَرْضَىٰٓ ﴿٥﴾

Kuma lalle ne, Ubangijinka zai yi ta bã ka kyauta sai ka yarda.

أَلَمْ يَجِدْكَ يَتِيمًۭا فَـَٔاوَىٰ ﴿٦﴾

Ashe, bai sãme ka marãya ba, sa'an nan Ya yi maka makõma?

وَوَجَدَكَ ضَآلًّۭا فَهَدَىٰ ﴿٧﴾

Kuma Ya sãme ka bã ka da shari'ã, sai Ya shiryar da kai?

وَوَجَدَكَ عَآئِلًۭا فَأَغْنَىٰ ﴿٨﴾

Kuma Ya sãme ka matalauci, sai Ya wadãtã ka?

فَأَمَّا ٱلْيَتِيمَ فَلَا تَقْهَرْ ﴿٩﴾

Sabõda haka, amma marãya, to, kada ka rinjãye shi.

وَأَمَّا ٱلسَّآئِلَ فَلَا تَنْهَرْ ﴿١٠﴾

Kuma amma mai tambaya, kada ka yi masa tsãwa.

وَأَمَّا بِنِعْمَةِ رَبِّكَ فَحَدِّثْ ﴿١١﴾

Kuma amma ni'imar Ubangijinka, sai ka faɗa (dõmin gõdiya).

أَلَمْ نَشْرَحْ لَكَ صَدْرَكَ ﴿١﴾

Ba Mu bũɗa maka zũciyarka ba (dõmin ɗaukar haƙuri da fahimta)?

وَوَضَعْنَا عَنكَ وِزْرَكَ ﴿٢﴾

Kuma Muka saryar maka da nauyinka, Ashe.

ٱلَّذِىٓ أَنقَضَ ظَهْرَكَ ﴿٣﴾

Wanda ya nauyayi bãyanka?

وَرَفَعْنَا لَكَ ذِكْرَكَ ﴿٤﴾

Kuma Muka ɗaukaka maka ambatonka?

فَإِنَّ مَعَ ٱلْعُسْرِ يُسْرًا ﴿٥﴾

To, lalle ne tãre da tsananin nan akwai wani sauƙi.

إِنَّ مَعَ ٱلْعُسْرِ يُسْرًۭا ﴿٦﴾

Lalle ne tãre da tsananin nan akwai wani sauƙi.

فَإِذَا فَرَغْتَ فَٱنصَبْ ﴿٧﴾

Sabõda haka idan ka ƙãre (ibãda) sai ka kafu (kana rõƙon Allah).

وَإِلَىٰ رَبِّكَ فَٱرْغَب ﴿٨﴾

Kuma zuwa ga Ubangijinka ka yi kwaɗayi.

بسم الله الرحمن الرحيم Jum 24 Muharram
الجمعة 24 محرّم
هلال متناقص Gajimaren Raguwa Rana 25 / 29.5
Haske 21%
Wata Sabo a cikin kwana 4
لا إله إلا الله Babu abin bautawa sai Allah