التين · Juz 30
Tafi zuwa
Alamomi
Mai karantawa / Qārī
Gudun sauti
Maimaita aya
Maimaita
Gungumewa kai
Fassara

Abubakar Mahmoud Gumi

Fontin larabci
Girman rubutu
Larabci
Fassara
Zangin da za a hadda
Maimaitawa
Kowane aya
Cikakken madauki
Babban mai karantawa
A ci gaba - Madauki A-B /

Kara Shafi 597 na Alkur'ani

Shafi 597 na Mushaf yana ɗauke da ayoyi 27. Yana cikin Juz 30, Hizb 60.

An sabunta a 10 Yuli 2026 03h52

Page 597 dans le Coran

27
ayoyi
30
Juz
60
Hizb
2
Surah
Juz 30
Shafi 597
سورة التين
Juz 30 75.5% (426/564)
Hizb 60 52.1% (150/288)

وَٱلتِّينِ وَٱلزَّيْتُونِ ﴿١﴾

Inã rantsuwa da Attinu da Azzaitũn.

وَطُورِ سِينِينَ ﴿٢﴾

Da Dũr Sĩnĩna.

وَهَـٰذَا ٱلْبَلَدِ ٱلْأَمِينِ ﴿٣﴾

Da wannan gari amintacce.

لَقَدْ خَلَقْنَا ٱلْإِنسَـٰنَ فِىٓ أَحْسَنِ تَقْوِيمٍۢ ﴿٤﴾

Lalle ne, Mun halitta mutum a cikin mafi kyawon tsayuwa.

ثُمَّ رَدَدْنَـٰهُ أَسْفَلَ سَـٰفِلِينَ ﴿٥﴾

Sa'an nan, Muka mayar da shi mafi ƙasƙantar masu rauni

إِلَّا ٱلَّذِينَ ءَامَنُوا۟ وَعَمِلُوا۟ ٱلصَّـٰلِحَـٰتِ فَلَهُمْ أَجْرٌ غَيْرُ مَمْنُونٍۢ ﴿٦﴾

Face waɗanda suka yi imani, kuma suka aikata ayyukan ƙwarai, saboda haka suna da sakamako wanda bã ya yankewa.

فَمَا يُكَذِّبُكَ بَعْدُ بِٱلدِّينِ ﴿٧﴾

To, bãyan haka mẽ ya sanya ka ka ƙaryata sakamako (wanda za a yi a bãyan Tãshin ¡iyãma)?

أَلَيْسَ ٱللَّهُ بِأَحْكَمِ ٱلْحَـٰكِمِينَ ﴿٨﴾

Ashe Allah bã Shi ne Mafi mãsu hukunci kyãwon hukunci ba?

ٱقْرَأْ بِٱسْمِ رَبِّكَ ٱلَّذِى خَلَقَ ﴿١﴾

Ka yi karatu da sunan Ubangijinka, wanda Ya yi halitta.

خَلَقَ ٱلْإِنسَـٰنَ مِنْ عَلَقٍ ﴿٢﴾

Ya hahitta mutum daga gudan jini.

ٱقْرَأْ وَرَبُّكَ ٱلْأَكْرَمُ ﴿٣﴾

Ka yi karatu, kuma UbangiJinka shi ne Mafi karimci.

ٱلَّذِى عَلَّمَ بِٱلْقَلَمِ ﴿٤﴾

Wanda Ya sanar (da mutum) game da alƙalami.

عَلَّمَ ٱلْإِنسَـٰنَ مَا لَمْ يَعْلَمْ ﴿٥﴾

Ya sanar da mutum abin da bai sani ba.

كَلَّآ إِنَّ ٱلْإِنسَـٰنَ لَيَطْغَىٰٓ ﴿٦﴾

A'aha! Lalle, ne mutum haƙĩƙa, yana girman kai (ya ƙi karatu).

أَن رَّءَاهُ ٱسْتَغْنَىٰٓ ﴿٧﴾

Dõmin yã ga kansa, yã wadãta.

إِنَّ إِلَىٰ رَبِّكَ ٱلرُّجْعَىٰٓ ﴿٨﴾

Lalle ne zuwa ga Ubangijinka makoma take.

أَرَءَيْتَ ٱلَّذِى يَنْهَىٰ ﴿٩﴾

Shin, kã ga wanda ke hana.

عَبْدًا إِذَا صَلَّىٰٓ ﴿١٠﴾

Bãwã idan yã yi salla?

أَرَءَيْتَ إِن كَانَ عَلَى ٱلْهُدَىٰٓ ﴿١١﴾

Ashe, kã gani, idan (shi bãwan) ya kasance a kan shiriya?

أَوْ أَمَرَ بِٱلتَّقْوَىٰٓ ﴿١٢﴾

Ko ya yi umurni da taƙawa?

أَرَءَيْتَ إِن كَذَّبَ وَتَوَلَّىٰٓ ﴿١٣﴾

Ashe, kã gani, idan (shi mai hanin) ya ƙaryata, kuma ya jũya bãya?

أَلَمْ يَعْلَم بِأَنَّ ٱللَّهَ يَرَىٰ ﴿١٤﴾

Ashe, bai sani ba cewa Allah Yanã gani?

كَلَّا لَئِن لَّمْ يَنتَهِ لَنَسْفَعًۢا بِٱلنَّاصِيَةِ ﴿١٥﴾

A'aha! Lalle ne, idan bai hanu ba, lalle ne zã Mu ja gãshin makwarkwaɗa.

نَاصِيَةٍۢ كَـٰذِبَةٍ خَاطِئَةٍۢ ﴿١٦﴾

Makwarkwaɗa maƙaryaciya, mai laifi.

فَلْيَدْعُ نَادِيَهُۥ ﴿١٧﴾

Sai ya kirayi ƙungiyarsa.

سَنَدْعُ ٱلزَّبَانِيَةَ ﴿١٨﴾

Zã Mu kirayi zabaniyãwa (mala'iku mãsu girma).

كَلَّا لَا تُطِعْهُ وَٱسْجُدْ وَٱقْتَرِب ۩ ﴿١٩﴾

A'aha kada ka bĩ shi. Kuma ka yi tawali'u, kuma ka nemi kusanta (zuwa ga Ubangijinka).

بسم الله الرحمن الرحيم Jum 24 Muharram
الجمعة 24 محرّم
هلال متناقص Gajimaren Raguwa Rana 25.1 / 29.5
Haske 21%
Wata Sabo a cikin kwana 4
حسبنا الله ونعم الوكيل Allah Ya isa mana, Shi ne mafi kyawun Mai Kiyaye