Ruku'u 511 daga Surah Al-Muddaththir ne (ayoyi 32 zuwa 56). Yana ɗauke da ayoyi 25 kuma yana cikin Juz 29.
An sabunta a 05 Agusta 2026 16h34
Karanta duka cikakken : Kara Ruku'u 511 na Alkur'ani →
كَلَّا وَٱلْقَمَرِ ﴿٣٢﴾
A'aha! Ina rantsuwa da watã.
وَٱلَّيْلِ إِذْ أَدْبَرَ ﴿٣٣﴾
Da dare a lõkacin da ya jũyar da baya.
وَٱلصُّبْحِ إِذَآ أَسْفَرَ ﴿٣٤﴾
Da sãfiya idan ta wãye.
إِنَّهَا لَإِحْدَى ٱلْكُبَرِ ﴿٣٥﴾
Ita (wutar) ɗayan manyan masĩfũ? ce.
نَذِيرًۭا لِّلْبَشَرِ ﴿٣٦﴾
Mai gargaɗĩ ce ga mutum.
لِمَن شَآءَ مِنكُمْ أَن يَتَقَدَّمَ أَوْ يَتَأَخَّرَ ﴿٣٧﴾
Ga wanda ya so, daga cikinku, ya gabãta ko ya jinkirta.
كُلُّ نَفْسٍۭ بِمَا كَسَبَتْ رَهِينَةٌ ﴿٣٨﴾
Kõwane rai ga abin da ya aikata jingina ce.
إِلَّآ أَصْحَـٰبَ ٱلْيَمِينِ ﴿٣٩﴾
Fãce mutãnen dãma.
فِى جَنَّـٰتٍۢ يَتَسَآءَلُونَ ﴿٤٠﴾
A cikin Aljanna suna tambayar jũna.
عَنِ ٱلْمُجْرِمِينَ ﴿٤١﴾
Game da mãsu laifi.
مَا سَلَكَكُمْ فِى سَقَرَ ﴿٤٢﴾
(Su ce musu) "Me ya shigar da ku a cikin Saƙar?"
قَالُوا۟ لَمْ نَكُ مِنَ ٱلْمُصَلِّينَ ﴿٤٣﴾
Suka ce: "Ba mu kasance munã a cikin mãsu salla ba."
وَلَمْ نَكُ نُطْعِمُ ٱلْمِسْكِينَ ﴿٤٤﴾
"Kuma ba mu kasance muna ciyar da matalautã ba."
وَكُنَّا نَخُوضُ مَعَ ٱلْخَآئِضِينَ ﴿٤٥﴾
"Kuma mun kasance muna kũtsãwa tãre da mãsu kũtsãwa."
وَكُنَّا نُكَذِّبُ بِيَوْمِ ٱلدِّينِ ﴿٤٦﴾
"Mun kasance munã ƙaryata rãnar sãkamako."
حَتَّىٰٓ أَتَىٰنَا ٱلْيَقِينُ ﴿٤٧﴾
"Har gaskiya (wãto mutuwa) ta zo mana."
فَمَا تَنفَعُهُمْ شَفَـٰعَةُ ٱلشَّـٰفِعِينَ ﴿٤٨﴾
Sabõda haka cẽton mãsu cẽto bã zai amfãne su ba.
فَمَا لَهُمْ عَنِ ٱلتَّذْكِرَةِ مُعْرِضِينَ ﴿٤٩﴾
Haba! Me ya same su, suka zama mãsu bijirewa daga wa'azin gaskiya.
كَأَنَّهُمْ حُمُرٌۭ مُّسْتَنفِرَةٌۭ ﴿٥٠﴾
Kamar dai sũ, jãkuna firgitattu ne.
فَرَّتْ مِن قَسْوَرَةٍۭ ﴿٥١﴾
Sun gudu daga zãki.
بَلْ يُرِيدُ كُلُّ ٱمْرِئٍۢ مِّنْهُمْ أَن يُؤْتَىٰ صُحُفًۭا مُّنَشَّرَةًۭ ﴿٥٢﴾
A'aha! Kõwãne mutum daga cikinsu yanã son a zo masa da takardu (da sũnansa) ana wãtsãwa
كَلَّا ۖ بَل لَّا يَخَافُونَ ٱلْـَٔاخِرَةَ ﴿٥٣﴾
A'aha! Kai dai, bã su jin tsõron Lãhira.
كَلَّآ إِنَّهُۥ تَذْكِرَةٌۭ ﴿٥٤﴾
A'aha! Lalle ne, shi (Alƙur'ãni) tunãtarwa ce.
فَمَن شَآءَ ذَكَرَهُۥ ﴿٥٥﴾
Dõmin wanda ya so, ya tuna.
وَمَا يَذْكُرُونَ إِلَّآ أَن يَشَآءَ ٱللَّهُ ۚ هُوَ أَهْلُ ٱلتَّقْوَىٰ وَأَهْلُ ٱلْمَغْفِرَةِ ﴿٥٦﴾
Kuma bã zã su tuna ba fãce idan Allah Ya so, Shi ne Ya cancanta a bi Shi da taƙawa kuma Ya cancanta ga Ya yi gãfara.