Abubakar Mahmoud Gumi
Ruku'u 511 daga Surah Al-Muddaththir ne (ayoyi 32 zuwa 56). Yana ɗauke da ayoyi 25 kuma yana cikin Juz 29.
An sabunta a 10 Yuli 2026 03h52
coran.read_full_page : Kara Ruku'u 511 na Alkur'ani →
فَمَا تَنفَعُهُمْ شَفَـٰعَةُ ٱلشَّـٰفِعِينَ ﴿٤٨﴾
Sabõda haka cẽton mãsu cẽto bã zai amfãne su ba.
فَمَا لَهُمْ عَنِ ٱلتَّذْكِرَةِ مُعْرِضِينَ ﴿٤٩﴾
Haba! Me ya same su, suka zama mãsu bijirewa daga wa'azin gaskiya.
كَأَنَّهُمْ حُمُرٌۭ مُّسْتَنفِرَةٌۭ ﴿٥٠﴾
Kamar dai sũ, jãkuna firgitattu ne.
فَرَّتْ مِن قَسْوَرَةٍۭ ﴿٥١﴾
Sun gudu daga zãki.
بَلْ يُرِيدُ كُلُّ ٱمْرِئٍۢ مِّنْهُمْ أَن يُؤْتَىٰ صُحُفًۭا مُّنَشَّرَةًۭ ﴿٥٢﴾
A'aha! Kõwãne mutum daga cikinsu yanã son a zo masa da takardu (da sũnansa) ana wãtsãwa
كَلَّا ۖ بَل لَّا يَخَافُونَ ٱلْـَٔاخِرَةَ ﴿٥٣﴾
A'aha! Kai dai, bã su jin tsõron Lãhira.
كَلَّآ إِنَّهُۥ تَذْكِرَةٌۭ ﴿٥٤﴾
A'aha! Lalle ne, shi (Alƙur'ãni) tunãtarwa ce.
فَمَن شَآءَ ذَكَرَهُۥ ﴿٥٥﴾
Dõmin wanda ya so, ya tuna.
وَمَا يَذْكُرُونَ إِلَّآ أَن يَشَآءَ ٱللَّهُ ۚ هُوَ أَهْلُ ٱلتَّقْوَىٰ وَأَهْلُ ٱلْمَغْفِرَةِ ﴿٥٦﴾
Kuma bã zã su tuna ba fãce idan Allah Ya so, Shi ne Ya cancanta a bi Shi da taƙawa kuma Ya cancanta ga Ya yi gãfara.