Abubakar Mahmoud Gumi
Ruku'u 520 daga Surah An-Naziat ne (ayoyi 1 zuwa 26). Yana ɗauke da ayoyi 26 kuma yana cikin Juz 30.
An sabunta a 10 Yuli 2026 03h52
coran.read_full_page : Kara Ruku'u 520 na Alkur'ani →
إِذْ نَادَىٰهُ رَبُّهُۥ بِٱلْوَادِ ٱلْمُقَدَّسِ طُوًى ﴿١٦﴾
A lõkacin da Ubangijinsa Ya kirãye shi, a cikin kwari mai tsarki, wato Duwã?
ٱذْهَبْ إِلَىٰ فِرْعَوْنَ إِنَّهُۥ طَغَىٰ ﴿١٧﴾
Ka tafi zuwa ga Fir'auna, lalle ne shi, ya ƙẽtare haddi.
فَقُلْ هَل لَّكَ إِلَىٰٓ أَن تَزَكَّىٰ ﴿١٨﴾
"Sai ka ce masa, Kõ zã ka so ka tsarkaka.
وَأَهْدِيَكَ إِلَىٰ رَبِّكَ فَتَخْشَىٰ ﴿١٩﴾
"Kuma in shiryar da kai zuwa ga Ubangijinka domin ka ji tsoronSa?"
فَأَرَىٰهُ ٱلْـَٔايَةَ ٱلْكُبْرَىٰ ﴿٢٠﴾
Sai ya nũna masa ãyar nan mafi girma.
فَكَذَّبَ وَعَصَىٰ ﴿٢١﴾
Sai ya ƙaryata, kuma ya sãɓa (umurni),
ثُمَّ أَدْبَرَ يَسْعَىٰ ﴿٢٢﴾
Sa'an nan ya jũya bãya, yanã tafiya da sauri.
فَحَشَرَ فَنَادَىٰ ﴿٢٣﴾
Sai ya yi gayya, sa'an nan ya yi kira.
فَقَالَ أَنَا۠ رَبُّكُمُ ٱلْأَعْلَىٰ ﴿٢٤﴾
Sai ya ce: "Nĩ ne Ubangijinku mafi ɗaudaka."
فَأَخَذَهُ ٱللَّهُ نَكَالَ ٱلْـَٔاخِرَةِ وَٱلْأُولَىٰٓ ﴿٢٥﴾
Sabõda haka Allah Ya kama shi, dõmin azãbar maganar ƙarshe da ta farko.
إِنَّ فِى ذَٰلِكَ لَعِبْرَةًۭ لِّمَن يَخْشَىٰٓ ﴿٢٦﴾
Lalle ne, a cikin wannan haƙiƙa akwai abin kula ga wanda yake tsõron Allah.