Kara Ruku'u 520 na Alkur'ani

Ruku'u 520 daga Surah An-Naziat ne (ayoyi 1 zuwa 26). Yana ɗauke da ayoyi 26 kuma yana cikin Juz 30.

An sabunta a 05 Agusta 2026 16h34

Ruku 520 a cikin Alkur'ani

26
ayoyi
1
Surah
30
Juz
v.1 – v.26
Ayoyi

Surori a cikin Ruku 520

النازعات · Juz 30
Shafi 583
Ruku'u 520
سورة النبإ
Juz 30 7.1% (40/564)
Hizb 59 14.5% (40/276)

وَٱلنَّـٰزِعَـٰتِ غَرْقًۭا ﴿١﴾

Ina rantsuwa da mala'iku mãsu fisgar rãyuka (na kafirai) da ƙarfi.

وَٱلنَّـٰشِطَـٰتِ نَشْطًۭا ﴿٢﴾

Da mãsu ɗibar rãyuka (na mũminai) da sauƙi a cikin nishãɗi.

وَٱلسَّـٰبِحَـٰتِ سَبْحًۭا ﴿٣﴾

Da mãsu sauka daga sama da umurnin Allah kamar suna iyo.

فَٱلسَّـٰبِقَـٰتِ سَبْقًۭا ﴿٤﴾

Sa'an nan, su zama mãsu gaugãwa (da umurnin Allah) kamar suna tsẽre.

فَٱلْمُدَبِّرَٰتِ أَمْرًۭا ﴿٥﴾

Sa, an nan, su kasance masu shirya gudanar da umurni.

يَوْمَ تَرْجُفُ ٱلرَّاجِفَةُ ﴿٦﴾

Rãnar da mai girgiza abũbuwa (bũsar farko) zã ta kaɗa.

تَتْبَعُهَا ٱلرَّادِفَةُ ﴿٧﴾

Mai biyar ta (bũsa ta biyu) nã biye.

قُلُوبٌۭ يَوْمَئِذٍۢ وَاجِفَةٌ ﴿٨﴾

Wasu zukãta, a rãnar nan, mãsu jin tsõro ne.

أَبْصَـٰرُهَا خَـٰشِعَةٌۭ ﴿٩﴾

Alhãli idãnunsu na ƙasƙantattu.

يَقُولُونَ أَءِنَّا لَمَرْدُودُونَ فِى ٱلْحَافِرَةِ ﴿١٠﴾

Sunã cẽwa "Ashe lalle zã a iya mayar da mu a kan sãwunmu?

أَءِذَا كُنَّا عِظَـٰمًۭا نَّخِرَةًۭ ﴿١١﴾

"Ashe, idan muka zama ƙasusuwa rududdugaggu?"

قَالُوا۟ تِلْكَ إِذًۭا كَرَّةٌ خَاسِرَةٌۭ ﴿١٢﴾

Suka ce: "Waccan kam kõmãwa ce, tãɓaɓɓiya!"

فَإِنَّمَا هِىَ زَجْرَةٌۭ وَٰحِدَةٌۭ ﴿١٣﴾

To, ita kam, tsãwa guda kawai ce.

فَإِذَا هُم بِٱلسَّاهِرَةِ ﴿١٤﴾

Sai kawai gã su a bãyan ƙasa.

هَلْ أَتَىٰكَ حَدِيثُ مُوسَىٰٓ ﴿١٥﴾

Shin, lãbãrin Mũsã ya zo maka?

إِذْ نَادَىٰهُ رَبُّهُۥ بِٱلْوَادِ ٱلْمُقَدَّسِ طُوًى ﴿١٦﴾

A lõkacin da Ubangijinsa Ya kirãye shi, a cikin kwari mai tsarki, wato Duwã?

ٱذْهَبْ إِلَىٰ فِرْعَوْنَ إِنَّهُۥ طَغَىٰ ﴿١٧﴾

Ka tafi zuwa ga Fir'auna, lalle ne shi, ya ƙẽtare haddi.

فَقُلْ هَل لَّكَ إِلَىٰٓ أَن تَزَكَّىٰ ﴿١٨﴾

"Sai ka ce masa, Kõ zã ka so ka tsarkaka.

وَأَهْدِيَكَ إِلَىٰ رَبِّكَ فَتَخْشَىٰ ﴿١٩﴾

"Kuma in shiryar da kai zuwa ga Ubangijinka domin ka ji tsoronSa?"

فَأَرَىٰهُ ٱلْـَٔايَةَ ٱلْكُبْرَىٰ ﴿٢٠﴾

Sai ya nũna masa ãyar nan mafi girma.

فَكَذَّبَ وَعَصَىٰ ﴿٢١﴾

Sai ya ƙaryata, kuma ya sãɓa (umurni),

ثُمَّ أَدْبَرَ يَسْعَىٰ ﴿٢٢﴾

Sa'an nan ya jũya bãya, yanã tafiya da sauri.

فَحَشَرَ فَنَادَىٰ ﴿٢٣﴾

Sai ya yi gayya, sa'an nan ya yi kira.

فَقَالَ أَنَا۠ رَبُّكُمُ ٱلْأَعْلَىٰ ﴿٢٤﴾

Sai ya ce: "Nĩ ne Ubangijinku mafi ɗaudaka."

فَأَخَذَهُ ٱللَّهُ نَكَالَ ٱلْـَٔاخِرَةِ وَٱلْأُولَىٰٓ ﴿٢٥﴾

Sabõda haka Allah Ya kama shi, dõmin azãbar maganar ƙarshe da ta farko.

إِنَّ فِى ذَٰلِكَ لَعِبْرَةًۭ لِّمَن يَخْشَىٰٓ ﴿٢٦﴾

Lalle ne, a cikin wannan haƙiƙa akwai abin kula ga wanda yake tsõron Allah.

بسم الله الرحمن الرحيم Lit 10 Rabi' al-Awwal
الاثنين 10 ربيع الأول
أحدب متزايد Cikakken Wata Tasowa Rana 11 / 29.5
Haske 85%
Cikakken Wata a cikin kwana 4
حسبنا الله ونعم الوكيل Allah Ya isa mana, Shi ne mafi kyawun Mai Kiyaye