Ruku'u 520 daga Surah An-Naziat ne (ayoyi 1 zuwa 26). Yana ɗauke da ayoyi 26 kuma yana cikin Juz 30.
An sabunta a 05 Agusta 2026 16h34
Karanta duka cikakken : Kara Ruku'u 520 na Alkur'ani →
وَٱلنَّـٰزِعَـٰتِ غَرْقًۭا ﴿١﴾
Ina rantsuwa da mala'iku mãsu fisgar rãyuka (na kafirai) da ƙarfi.
وَٱلنَّـٰشِطَـٰتِ نَشْطًۭا ﴿٢﴾
Da mãsu ɗibar rãyuka (na mũminai) da sauƙi a cikin nishãɗi.
وَٱلسَّـٰبِحَـٰتِ سَبْحًۭا ﴿٣﴾
Da mãsu sauka daga sama da umurnin Allah kamar suna iyo.
فَٱلسَّـٰبِقَـٰتِ سَبْقًۭا ﴿٤﴾
Sa'an nan, su zama mãsu gaugãwa (da umurnin Allah) kamar suna tsẽre.
فَٱلْمُدَبِّرَٰتِ أَمْرًۭا ﴿٥﴾
Sa, an nan, su kasance masu shirya gudanar da umurni.
يَوْمَ تَرْجُفُ ٱلرَّاجِفَةُ ﴿٦﴾
Rãnar da mai girgiza abũbuwa (bũsar farko) zã ta kaɗa.
تَتْبَعُهَا ٱلرَّادِفَةُ ﴿٧﴾
Mai biyar ta (bũsa ta biyu) nã biye.
قُلُوبٌۭ يَوْمَئِذٍۢ وَاجِفَةٌ ﴿٨﴾
Wasu zukãta, a rãnar nan, mãsu jin tsõro ne.
أَبْصَـٰرُهَا خَـٰشِعَةٌۭ ﴿٩﴾
Alhãli idãnunsu na ƙasƙantattu.
يَقُولُونَ أَءِنَّا لَمَرْدُودُونَ فِى ٱلْحَافِرَةِ ﴿١٠﴾
Sunã cẽwa "Ashe lalle zã a iya mayar da mu a kan sãwunmu?
أَءِذَا كُنَّا عِظَـٰمًۭا نَّخِرَةًۭ ﴿١١﴾
"Ashe, idan muka zama ƙasusuwa rududdugaggu?"
قَالُوا۟ تِلْكَ إِذًۭا كَرَّةٌ خَاسِرَةٌۭ ﴿١٢﴾
Suka ce: "Waccan kam kõmãwa ce, tãɓaɓɓiya!"
فَإِنَّمَا هِىَ زَجْرَةٌۭ وَٰحِدَةٌۭ ﴿١٣﴾
To, ita kam, tsãwa guda kawai ce.
فَإِذَا هُم بِٱلسَّاهِرَةِ ﴿١٤﴾
Sai kawai gã su a bãyan ƙasa.
هَلْ أَتَىٰكَ حَدِيثُ مُوسَىٰٓ ﴿١٥﴾
Shin, lãbãrin Mũsã ya zo maka?
إِذْ نَادَىٰهُ رَبُّهُۥ بِٱلْوَادِ ٱلْمُقَدَّسِ طُوًى ﴿١٦﴾
A lõkacin da Ubangijinsa Ya kirãye shi, a cikin kwari mai tsarki, wato Duwã?
ٱذْهَبْ إِلَىٰ فِرْعَوْنَ إِنَّهُۥ طَغَىٰ ﴿١٧﴾
Ka tafi zuwa ga Fir'auna, lalle ne shi, ya ƙẽtare haddi.
فَقُلْ هَل لَّكَ إِلَىٰٓ أَن تَزَكَّىٰ ﴿١٨﴾
"Sai ka ce masa, Kõ zã ka so ka tsarkaka.
وَأَهْدِيَكَ إِلَىٰ رَبِّكَ فَتَخْشَىٰ ﴿١٩﴾
"Kuma in shiryar da kai zuwa ga Ubangijinka domin ka ji tsoronSa?"
فَأَرَىٰهُ ٱلْـَٔايَةَ ٱلْكُبْرَىٰ ﴿٢٠﴾
Sai ya nũna masa ãyar nan mafi girma.
فَكَذَّبَ وَعَصَىٰ ﴿٢١﴾
Sai ya ƙaryata, kuma ya sãɓa (umurni),
ثُمَّ أَدْبَرَ يَسْعَىٰ ﴿٢٢﴾
Sa'an nan ya jũya bãya, yanã tafiya da sauri.
فَحَشَرَ فَنَادَىٰ ﴿٢٣﴾
Sai ya yi gayya, sa'an nan ya yi kira.
فَقَالَ أَنَا۠ رَبُّكُمُ ٱلْأَعْلَىٰ ﴿٢٤﴾
Sai ya ce: "Nĩ ne Ubangijinku mafi ɗaudaka."
فَأَخَذَهُ ٱللَّهُ نَكَالَ ٱلْـَٔاخِرَةِ وَٱلْأُولَىٰٓ ﴿٢٥﴾
Sabõda haka Allah Ya kama shi, dõmin azãbar maganar ƙarshe da ta farko.
إِنَّ فِى ذَٰلِكَ لَعِبْرَةًۭ لِّمَن يَخْشَىٰٓ ﴿٢٦﴾
Lalle ne, a cikin wannan haƙiƙa akwai abin kula ga wanda yake tsõron Allah.