عبس · Juz 30
Tafi zuwa
Alamomi
Mai karantawa / Qārī
Gudun sauti
Maimaita aya
Maimaita
Gungumewa kai
Fassara

Abubakar Mahmoud Gumi

Fontin larabci
Girman rubutu
Larabci
Fassara
Zangin da za a hadda
Maimaitawa
Kowane aya
Cikakken madauki
Babban mai karantawa
A ci gaba - Madauki A-B /

Kara Surah Abasa

Surah Abasa (عبس) ita ce surah na Makka ta Alkur'ani tana da ayoyi 42. Ku karanta, ku saurari kuma ku hadda wannan surah tare da kayanmu masu hulɗa.

An sabunta a 10 Yuli 2026 03h52

📖 Karatu minti 1

Surah Abasa cikin lambobi

Tsarin saukarwa
Saukarwa n° 17 / 114
(na Makka)
133
kalmomi
-81.5% vs matsakaici
599
haruffa
-80.5% vs matsakaici
1
min karantawa
42
ayoyi
-23.2% vs matsakaici

Yawan amfani da kalmomin bincike في سورة Abasa

الله 0
رب 0

Haruffa da yawa suke fitowa في سورة Abasa

م
43
#1
ا
42
#2
ل
35
#3
ه
35
#4
ن
33
#5
Kara Surah Abasa
سورة عبس
Juz 30 15.2% (86/564)
Hizb 59 31.2% (86/276)

عَبَسَ وَتَوَلَّىٰٓ ﴿١﴾

Yã game huska kuma ya jũya bãya.

أَن جَآءَهُ ٱلْأَعْمَىٰ ﴿٢﴾

Sabõda makãho yã je masa.

وَمَا يُدْرِيكَ لَعَلَّهُۥ يَزَّكَّىٰٓ ﴿٣﴾

To, me ya sanar da kai cẽwa watakila shi ne zai tsarkaka.

أَوْ يَذَّكَّرُ فَتَنفَعَهُ ٱلذِّكْرَىٰٓ ﴿٤﴾

Ko ya tuna, dõmin tunãwar ta amfane shi?

أَمَّا مَنِ ٱسْتَغْنَىٰ ﴿٥﴾

Amma wanda ya wadãtu da dũkiya.

فَأَنتَ لَهُۥ تَصَدَّىٰ ﴿٦﴾

Sa'an nan kai kuma ka ɗora bijira zuwa gare shi!

وَمَا عَلَيْكَ أَلَّا يَزَّكَّىٰ ﴿٧﴾

To, me zai cũce ka idan bai tsarkaka ba?

وَأَمَّا مَن جَآءَكَ يَسْعَىٰ ﴿٨﴾

Kuma, amma wanda ya zomaka yana gaugãwa.

وَهُوَ يَخْشَىٰ ﴿٩﴾

Alhãli shĩ yanã jin tsõrõn Allah.

فَأَنتَ عَنْهُ تَلَهَّىٰ ﴿١٠﴾

Kai kuma kã shagala ga barinsa!

كَلَّآ إِنَّهَا تَذْكِرَةٌۭ ﴿١١﴾

A'aha! Lalle ne, wannan tunãtarwa ce.

فَمَن شَآءَ ذَكَرَهُۥ ﴿١٢﴾

Sabõda wanda ya so ya tunaShi (Allah).

فِى صُحُفٍۢ مُّكَرَّمَةٍۢ ﴿١٣﴾

(Tunãtarwa ce) ta cikin littafai abãban girmamãwa,

مَّرْفُوعَةٍۢ مُّطَهَّرَةٍۭ ﴿١٤﴾

Abãban ɗaukakãwa, abãban tsarkakẽwa.

بِأَيْدِى سَفَرَةٍۢ ﴿١٥﴾

A cikin hannãyen mala'iku marubũta.

كِرَامٍۭ بَرَرَةٍۢ ﴿١٦﴾

Mãsu daraja, mãsu ɗã'a ga Allah.

قُتِلَ ٱلْإِنسَـٰنُ مَآ أَكْفَرَهُۥ ﴿١٧﴾

An la'ani mutum (kafiri). Mẽ yã yi kãfircinsa!

مِنْ أَىِّ شَىْءٍ خَلَقَهُۥ ﴿١٨﴾

Daga wane abu, (Allah) Ya halitta shi?

مِن نُّطْفَةٍ خَلَقَهُۥ فَقَدَّرَهُۥ ﴿١٩﴾

Daga ɗigon maniyyi, Ya halitta shi sa'an nan Ya ƙaddarã shi (ga halaye).

ثُمَّ ٱلسَّبِيلَ يَسَّرَهُۥ ﴿٢٠﴾

Sa'an nan, hanyarsa ta fita Ya sauƙaƙe masa.

ثُمَّ أَمَاتَهُۥ فَأَقْبَرَهُۥ ﴿٢١﴾

Sa'an nan, Ya matar da shi sai Ya sanya shi a cikin kabari.

ثُمَّ إِذَا شَآءَ أَنشَرَهُۥ ﴿٢٢﴾

Sa'an nan, idan Ya so lalle ne zai tãyar da shi.

كَلَّا لَمَّا يَقْضِ مَآ أَمَرَهُۥ ﴿٢٣﴾

Haƙĩƙa bai i da aikata abin da Allah Ya umurce shi ba (lõkacin sanya shi a cikin kabari).

فَلْيَنظُرِ ٱلْإِنسَـٰنُ إِلَىٰ طَعَامِهِۦٓ ﴿٢٤﴾

To, mutum ya dũba zuwa ga abincinsa.

أَنَّا صَبَبْنَا ٱلْمَآءَ صَبًّۭا ﴿٢٥﴾

Lalle ne Mũ, Mun zuo ruwa, zubõwa.

ثُمَّ شَقَقْنَا ٱلْأَرْضَ شَقًّۭا ﴿٢٦﴾

Sa'an nan, Muka tsattsãge ƙasa tsattsagewa.

فَأَنۢبَتْنَا فِيهَا حَبًّۭا ﴿٢٧﴾

Sa'an nan, Muka tsirar da ƙwaya, a cikinta.

وَعِنَبًۭا وَقَضْبًۭا ﴿٢٨﴾

Da inabi da ciyãwa.

وَزَيْتُونًۭا وَنَخْلًۭا ﴿٢٩﴾

Da zaitũni da itãcen dabĩno.

وَحَدَآئِقَ غُلْبًۭا ﴿٣٠﴾

Da lambuna, mãsu yawan itãce.

وَفَـٰكِهَةًۭ وَأَبًّۭا ﴿٣١﴾

Da 'yã'yan itãcen marmari, da makiyãyã ta dabbõbi.

مَّتَـٰعًۭا لَّكُمْ وَلِأَنْعَـٰمِكُمْ ﴿٣٢﴾

Domin jin dãɗi a gare ku, ku da dabbobinku.

فَإِذَا جَآءَتِ ٱلصَّآخَّةُ ﴿٣٣﴾

To, idan mai tsãwa (busa ta biyu) ta zo.

يَوْمَ يَفِرُّ ٱلْمَرْءُ مِنْ أَخِيهِ ﴿٣٤﴾

Rãnar da mutum yake gudu daga ɗan'uwansa.

وَأُمِّهِۦ وَأَبِيهِ ﴿٣٥﴾

Da uwarsa da ubansa.

وَصَـٰحِبَتِهِۦ وَبَنِيهِ ﴿٣٦﴾

Da mãtarsa da ɗiyansa.

لِكُلِّ ٱمْرِئٍۢ مِّنْهُمْ يَوْمَئِذٍۢ شَأْنٌۭ يُغْنِيهِ ﴿٣٧﴾

Ga kõwane mutum daga cikinsu, a rãnar nan akwai wani sha'ani da ya ishe shi.

وُجُوهٌۭ يَوْمَئِذٍۢ مُّسْفِرَةٌۭ ﴿٣٨﴾

Wasu huskõki, a rãnar nan, mãsu haske ne.

ضَاحِكَةٌۭ مُّسْتَبْشِرَةٌۭ ﴿٣٩﴾

Mãsu dãriya ne, mãsu bushãra.

وَوُجُوهٌۭ يَوْمَئِذٍ عَلَيْهَا غَبَرَةٌۭ ﴿٤٠﴾

Wasu huskõki, a rãnar nan, akwai ƙũra a kansu.

تَرْهَقُهَا قَتَرَةٌ ﴿٤١﴾

Baƙi zai rufe su.

أُو۟لَـٰٓئِكَ هُمُ ٱلْكَفَرَةُ ٱلْفَجَرَةُ ﴿٤٢﴾

Waɗannan sũ ne kãfirai fãjirai (ga ayyukansu).

بسم الله الرحمن الرحيم Jum 24 Muharram
الجمعة 24 محرّم
هلال متناقص Gajimaren Raguwa Rana 25.1 / 29.5
Haske 21%
Wata Sabo a cikin kwana 4
سبحان الله Subhanallah - Tsarkin Allah